• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Damke Wani Mutum Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

by Sadiq
2 years ago
Adamawa

Rundunar ‘yansandan Jihar Adamawa ta cafke wani magidanci mai suna Aminu Abubakar mai shekara 56 bisa laifin kashe matarsa.

Abubakar, mazaunin Lelewaji, a yankin Shagari Phase 2 a Yola, a karamar hukumar Yola ta Kudu a jihar, an zargin ya yi wa matarsa ​​Nana Fadimatu dukan tsiya wanda ya yi ajalinta har lahira, bayan ya fahimci shirinta na auren wani mutum.

  • Alkawarin Da Tinubu Ya Yi Wa Ma’aikatan Gwamnati
  • Batun Sake Nazarin Dakatar Da Tsohon Sarkin Kano…

Ana zargin Abubakar da sakin mamaciyar har sau biyu tare da ba ta masauki ba, har zuwa lokacin da za a sasanta auren.

Amma kafin su sasanta, an ce marigayiyar na shirin auren wani mutum, lamarin da ya harzuka Abubakar, inda ya shiga tashin hankali.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce, “Wanda ake zargin, Aminu Abubakar, mazaunin Lelewaji, Shagari Phase 2, a karamar hukumar Yola ta Kudu, ya yi wa marigayiya Nana Fadimatu dukan tsiya bayan wata ‘yar rashin jituwa da ta barke tsakaninsu lokacin da ya ji labarin cewa marigayiyar za ta auri wani daban.

LABARAI MASU NASABA

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

“Wanda ake zargin ya fusata ya danne ta a ranar 5/5/2023 da misalin karfe 10 na dare, inda ya buge ta da karfi ta hanyar buga mata wani abu mai kauri sakamakon hakan ta fadi a sume sannan aka sanar da cewa ta mutu.

“’Yansanda sun kama wanda ake zargin ne a hedikwatar ‘yansanda ta Shagari sakamakon rahoton da aka samu daga sabon angon nata, Mahmud Rufa’i na Shagari a karamar hukumar Yola ta Kudu.

“Bincike ya zuwa yanzu ya nuna cewa wanda ake zargin shi ne manajan kamfanin ruwa na Anasam a gidan Jambutu 50 yana da ’ya daya tare da marigayiyar bayan shekaru tara da aurensu.

“Kwamishanan ‘yansanda CP Afolabi Babatola yayin da yake bayyana kaduwarsa ya yaba wa DPO din Shagari bisa kama wanda ake zargin.”

Ya kara da cewa CP din ya umarci jami’an sashen yaki da kisan kai da ke ma’aikatan CID na jihar da su dauki nauyin gudanar da bincike tare da tabbatar da cewa doka ta yi aiki.

Haka zalika ya yi kira ga jama’ar yankin da su rika kai rahoton mutanen da ba su da alaka da su a unguwanninsu ga ‘yansanda.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Adamawa
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Next Post
Sin: Za A Harba Kumbon Jigilar Kaya Samfurin Tianzhou-6

Sin: Za A Harba Kumbon Jigilar Kaya Samfurin Tianzhou-6

LABARAI MASU NASABA

Adamawa

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.