• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Yi Artabu Da Masu Garkuwa Da Mutane A Abuja

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
‘Yansanda Sun Yi Artabu Da Masu Garkuwa Da Mutane A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja sun kama wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne bayan wani kazamin fada da suka yi da ‘yan bindiga.

Wasu gungun masu garkuwa da mutane sun kai farmaki wani gida a unguwar Kubwa da ke Babban Birnin Tarayya Abuja da sanyin safiya bayan da suka gamu da ‘yansanda, inda suka bude wuta tare da gudu zuwa wata fadama da ke kusa.

  • Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai
  • Tsohon Shugaban INEC, Farfesa Humphrey Nwosu Ya Rasu

Wakilinmu ya ruwaito cewa ‘yansandan sun bi sawun barayin, inda suka kama daya daga cikinsu tare da kwato wata motar gungun barayin.

Da aka tuntubi kwamishinan ‘yan sandan Babban Birnin Tarayya Abuja, Tunji Disu, ya tabbatar da cewa an kama daya daga cikin masu garkuwa da mutanen tare da kwace makamin dake hannunsa.

Ya ce ‘yan sandan sun yi gaggawar kai dauki ne saboda kiran da daya daga cikin mazauna yankin ya yi.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Disu ya bukaci mazauna yankin da su gaggauta tuntubar layukan gaggawa na rundunar a duk lokacin da suka ga abubuwan da ba su dace ba a muhallinsu.

Ya ce, “An yi sa’a an kama daya daga cikinsu, wasu kuma sun tsere. Sannan kuma mun kwato musu bindiga kirar AK-47 da harsashi mai rai guda 20, da bindigar Beretta da harsashi 12 a cikinta.

“Muna kokarin kama wasu da suka tsere. Yana da mahimmanci a lura cewa muna so mu gode wa wadanda suka ga lamarin kuma suka kira ‘yan sanda da sauri.

Muna rokon jama’a kada su tsaya jira yayin da suka ga wani da zai kawo rashin zaman lafiya ba tare da daukar mataki ba. Su yi la’akari da duk wani mataki da ke faruwa, da zarar sun ga wani yanayi da ya yi kama da fashi, su kira shashen gaggawa ‘yan sanda za su kawo daukin gaggawa.

“Don haka ina so in gode wa wanda ya kira mu mu dauki matakin gaggawa. Zan yi iyakacin kokarina domin nemo wadanda da suka tsere daga wurin da lamarin ya faru don neman mafaka. “


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaAbujaArtabuMasu Garkuwa Da Mutane
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Naɗa Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Next Post

An Cafke Wasu Matasa Da Laifin Fashin Wayoyi A Bauchi

Related

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

1 day ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

1 day ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

1 week ago
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

1 week ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

1 month ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

1 month ago
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

An Cafke Wasu Matasa Da Laifin Fashin Wayoyi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.