ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Yi Artabu Da Masu Garkuwa Da Mutane A Abuja

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Artabu

Jami’an rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja sun kama wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne bayan wani kazamin fada da suka yi da ‘yan bindiga.

Wasu gungun masu garkuwa da mutane sun kai farmaki wani gida a unguwar Kubwa da ke Babban Birnin Tarayya Abuja da sanyin safiya bayan da suka gamu da ‘yansanda, inda suka bude wuta tare da gudu zuwa wata fadama da ke kusa.

  • Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai
  • Tsohon Shugaban INEC, Farfesa Humphrey Nwosu Ya Rasu

Wakilinmu ya ruwaito cewa ‘yansandan sun bi sawun barayin, inda suka kama daya daga cikinsu tare da kwato wata motar gungun barayin.

ADVERTISEMENT

Da aka tuntubi kwamishinan ‘yan sandan Babban Birnin Tarayya Abuja, Tunji Disu, ya tabbatar da cewa an kama daya daga cikin masu garkuwa da mutanen tare da kwace makamin dake hannunsa.

Ya ce ‘yan sandan sun yi gaggawar kai dauki ne saboda kiran da daya daga cikin mazauna yankin ya yi.

LABARAI MASU NASABA

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

Disu ya bukaci mazauna yankin da su gaggauta tuntubar layukan gaggawa na rundunar a duk lokacin da suka ga abubuwan da ba su dace ba a muhallinsu.

Ya ce, “An yi sa’a an kama daya daga cikinsu, wasu kuma sun tsere. Sannan kuma mun kwato musu bindiga kirar AK-47 da harsashi mai rai guda 20, da bindigar Beretta da harsashi 12 a cikinta.

“Muna kokarin kama wasu da suka tsere. Yana da mahimmanci a lura cewa muna so mu gode wa wadanda suka ga lamarin kuma suka kira ‘yan sanda da sauri.

Muna rokon jama’a kada su tsaya jira yayin da suka ga wani da zai kawo rashin zaman lafiya ba tare da daukar mataki ba. Su yi la’akari da duk wani mataki da ke faruwa, da zarar sun ga wani yanayi da ya yi kama da fashi, su kira shashen gaggawa ‘yan sanda za su kawo daukin gaggawa.

“Don haka ina so in gode wa wanda ya kira mu mu dauki matakin gaggawa. Zan yi iyakacin kokarina domin nemo wadanda da suka tsere daga wurin da lamarin ya faru don neman mafaka. “

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari
Kotu Da Ɗansanda

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

An Cafke Wasu Matasa Da Laifin Fashin Wayoyi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.