• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Yi Artabu Da Masu Garkuwa Da Mutane A Abuja

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
‘Yansanda Sun Yi Artabu Da Masu Garkuwa Da Mutane A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an rundunar ‘yansandan Babban Birnin Tarayya Abuja sun kama wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne bayan wani kazamin fada da suka yi da ‘yan bindiga.

Wasu gungun masu garkuwa da mutane sun kai farmaki wani gida a unguwar Kubwa da ke Babban Birnin Tarayya Abuja da sanyin safiya bayan da suka gamu da ‘yansanda, inda suka bude wuta tare da gudu zuwa wata fadama da ke kusa.

  • Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai
  • Tsohon Shugaban INEC, Farfesa Humphrey Nwosu Ya Rasu

Wakilinmu ya ruwaito cewa ‘yansandan sun bi sawun barayin, inda suka kama daya daga cikinsu tare da kwato wata motar gungun barayin.

Da aka tuntubi kwamishinan ‘yan sandan Babban Birnin Tarayya Abuja, Tunji Disu, ya tabbatar da cewa an kama daya daga cikin masu garkuwa da mutanen tare da kwace makamin dake hannunsa.

Ya ce ‘yan sandan sun yi gaggawar kai dauki ne saboda kiran da daya daga cikin mazauna yankin ya yi.

Labarai Masu Nasaba

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

Disu ya bukaci mazauna yankin da su gaggauta tuntubar layukan gaggawa na rundunar a duk lokacin da suka ga abubuwan da ba su dace ba a muhallinsu.

Ya ce, “An yi sa’a an kama daya daga cikinsu, wasu kuma sun tsere. Sannan kuma mun kwato musu bindiga kirar AK-47 da harsashi mai rai guda 20, da bindigar Beretta da harsashi 12 a cikinta.

“Muna kokarin kama wasu da suka tsere. Yana da mahimmanci a lura cewa muna so mu gode wa wadanda suka ga lamarin kuma suka kira ‘yan sanda da sauri.

Muna rokon jama’a kada su tsaya jira yayin da suka ga wani da zai kawo rashin zaman lafiya ba tare da daukar mataki ba. Su yi la’akari da duk wani mataki da ke faruwa, da zarar sun ga wani yanayi da ya yi kama da fashi, su kira shashen gaggawa ‘yan sanda za su kawo daukin gaggawa.

“Don haka ina so in gode wa wanda ya kira mu mu dauki matakin gaggawa. Zan yi iyakacin kokarina domin nemo wadanda da suka tsere daga wurin da lamarin ya faru don neman mafaka. “


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaAbujaArtabuMasu Garkuwa Da Mutane
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Naɗa Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Next Post

An Cafke Wasu Matasa Da Laifin Fashin Wayoyi A Bauchi

Related

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

1 week ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

4 weeks ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

4 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

1 month ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

An Cafke Wasu Matasa Da Laifin Fashin Wayoyi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

August 7, 2025
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

August 7, 2025
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 7, 2025
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

August 7, 2025
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

August 7, 2025
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

August 7, 2025
Neja

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

August 7, 2025
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

August 7, 2025
Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.