• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Tana Kasa Tana Dabo

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
in Kasashen Ketare
0
Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Tana Kasa Tana Dabo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Antony Blinken ya sauka a Katar domin tabbatar da yarjejeniyar tsagaita bude wutar a Gaza da kuma sakin mutanen da aka yi garkuwa da su wadda a yanzu haka take kasa take dabo tun bayan martanin kungiyar Hamas.

Rahotanni dai sun ce tun tsakar dare mista Blinken ya farka daga barci yake ta nazarin sakon da Hamas ta mika wa Katar da Egypt masu shiga tsakani.

Kungiyar Hamas dai ta ce a shirye take ta yi maraba da yarjejeniyar to amma ta sa sharadin cewa sai idan Isra’ila ta amince da dakatar da yaki baki dayansa.

  • Daga Karshe, Biden Ya Zamanto Irinsu Trump
  • Ba Za A Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gaza Ba Har Sai Amurka Ta Daina Samarwa Isra’ila Da Makamai

Gwamnatin Isra’ila dai ba ta mayar da martani ba amma kuma wani jami’in Isra’ilar wanda ba ya son a ambaci sunansa ya ce sauyin da Hamas ke son yi ga yarjejeniyar tamkar watsi da ita ne.

BBC na daga cikin tawagar ‘yan jaridar da ke tafiya da mista Blinken a ziyarar tasa zu-wa Birnin Doha inda yake ganawa da shugabannin Katar domin tabbatar da yarjejeni-yar ba ta samu cikas ba.

Labarai Masu Nasaba

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

A ranar Talata dai Mista Blinken da firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu sun kara nanata muhimmancin yarjejeniyar duk da cewa Mista Netanyahu bai fito fili ya yi maraba da yarjejeniyar ba wadda shugaban Amurka, Joe Biden ya ce Isra’ilar ce ta fito da ita.

Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Amurka, John Kirby ya ce ana duba martanin na Ha-mas. Kungiyar dai ta ce za ta hau teburin sulhu da zuciya daya.

“Mun karbi maratanin Hamas da ta gabatar ta hannun Katar da Egypt muna kuma nazartarsa yanzu haka kuma ina tunanin cewar iya abin da za mu iya yi kenan yanzu, tun da mun sami wannan martanin a hannun yanzu, kuma za mu yi aiki a kansa,” in ji Kirby.

Wakiliyar BBC ta ce wani jami’in Hamas Aze Tariksh ya ce martanin na su ya bude kofar cimma yarjrjeniya.

To amma wani jami’in Isra’ila da ya nemi a sakaye sunansa ya zargi Hamas da sauya wasu muhimman sassa na daftarin yarjejeniyar, kuma haka a wajensu, tamkar ta yi watsi da yarjejeniyar ne.

Jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya ta ce amincewa da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya yi, wani mataki ne na goyon bayan samar da zaman lafiya.

Linda Thomas-Greenfield ta ce kasashen duniya sun hada kai kan yarjejeniyar da za ta ceci rayuka, da mayar da mutanen Isra’ila da aka yi garkuwa da su gida da kuma taimaka wa fararen hula Falasdinawa.

A rubuce dai kudurin na nuna cewa Isra’ila ta amince da yarjejeniyar wadda shugaba Biden ya sanar a watan jiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EgyptGazaGazzaIsraelUnited Nations
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jiragen Dakon Kaya Masu Zirga-zirga Tsakanin Sin Da Turai Sun Gudanar Da Zirga-zirga Mafi Yawa A Mayu

Next Post

Sallah: Tinubu Ya Bukaci Hadin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin ‘Yan Nijeriya

Related

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

22 hours ago
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci
Kasashen Ketare

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

2 days ago
Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

7 days ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan HulÉ—a
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan HulÉ—a

1 week ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

1 week ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

2 weeks ago
Next Post
Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya

Sallah: Tinubu Ya Bukaci Hadin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.