• English
  • Business News
Monday, September 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Tana Kasa Tana Dabo

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Tana Kasa Tana Dabo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Antony Blinken ya sauka a Katar domin tabbatar da yarjejeniyar tsagaita bude wutar a Gaza da kuma sakin mutanen da aka yi garkuwa da su wadda a yanzu haka take kasa take dabo tun bayan martanin kungiyar Hamas.

Rahotanni dai sun ce tun tsakar dare mista Blinken ya farka daga barci yake ta nazarin sakon da Hamas ta mika wa Katar da Egypt masu shiga tsakani.

Kungiyar Hamas dai ta ce a shirye take ta yi maraba da yarjejeniyar to amma ta sa sharadin cewa sai idan Isra’ila ta amince da dakatar da yaki baki dayansa.

  • Daga Karshe, Biden Ya Zamanto Irinsu Trump
  • Ba Za A Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gaza Ba Har Sai Amurka Ta Daina Samarwa Isra’ila Da Makamai

Gwamnatin Isra’ila dai ba ta mayar da martani ba amma kuma wani jami’in Isra’ilar wanda ba ya son a ambaci sunansa ya ce sauyin da Hamas ke son yi ga yarjejeniyar tamkar watsi da ita ne.

BBC na daga cikin tawagar ‘yan jaridar da ke tafiya da mista Blinken a ziyarar tasa zu-wa Birnin Doha inda yake ganawa da shugabannin Katar domin tabbatar da yarjejeni-yar ba ta samu cikas ba.

Labarai Masu Nasaba

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

A ranar Talata dai Mista Blinken da firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu sun kara nanata muhimmancin yarjejeniyar duk da cewa Mista Netanyahu bai fito fili ya yi maraba da yarjejeniyar ba wadda shugaban Amurka, Joe Biden ya ce Isra’ilar ce ta fito da ita.

Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Amurka, John Kirby ya ce ana duba martanin na Ha-mas. Kungiyar dai ta ce za ta hau teburin sulhu da zuciya daya.

“Mun karbi maratanin Hamas da ta gabatar ta hannun Katar da Egypt muna kuma nazartarsa yanzu haka kuma ina tunanin cewar iya abin da za mu iya yi kenan yanzu, tun da mun sami wannan martanin a hannun yanzu, kuma za mu yi aiki a kansa,” in ji Kirby.

Wakiliyar BBC ta ce wani jami’in Hamas Aze Tariksh ya ce martanin na su ya bude kofar cimma yarjrjeniya.

To amma wani jami’in Isra’ila da ya nemi a sakaye sunansa ya zargi Hamas da sauya wasu muhimman sassa na daftarin yarjejeniyar, kuma haka a wajensu, tamkar ta yi watsi da yarjejeniyar ne.

Jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya ta ce amincewa da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya yi, wani mataki ne na goyon bayan samar da zaman lafiya.

Linda Thomas-Greenfield ta ce kasashen duniya sun hada kai kan yarjejeniyar da za ta ceci rayuka, da mayar da mutanen Isra’ila da aka yi garkuwa da su gida da kuma taimaka wa fararen hula Falasdinawa.

A rubuce dai kudurin na nuna cewa Isra’ila ta amince da yarjejeniyar wadda shugaba Biden ya sanar a watan jiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EgyptGazaGazzaIsraelUnited Nations
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jiragen Dakon Kaya Masu Zirga-zirga Tsakanin Sin Da Turai Sun Gudanar Da Zirga-zirga Mafi Yawa A Mayu

Next Post

Sallah: Tinubu Ya Bukaci Hadin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin ‘Yan Nijeriya

Related

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan
Kasashen Ketare

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

3 hours ago
Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi
Kasashen Ketare

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

4 days ago
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida
Kasashen Ketare

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

7 days ago
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

1 week ago
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda
Kasashen Ketare

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

1 week ago
An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa
Kasashen Ketare

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

2 weeks ago
Next Post
Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya

Sallah: Tinubu Ya Bukaci Hadin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba ÆŠaya

Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba ÆŠaya

September 1, 2025
Ƴansanda Sun Gano Motocin Sata 2 A Adamawa

Ƴansanda Sun Gano Motocin Sata 2 A Adamawa

September 1, 2025
Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

September 1, 2025
Isak Na Dab Da Zama ÆŠan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya

Isak Na Dab Da Zama ÆŠan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya

September 1, 2025
Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

September 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

September 1, 2025
Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai

September 1, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

August 31, 2025
Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

August 31, 2025
Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

August 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.