ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Tana Kasa Tana Dabo

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Gaza

Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Antony Blinken ya sauka a Katar domin tabbatar da yarjejeniyar tsagaita bude wutar a Gaza da kuma sakin mutanen da aka yi garkuwa da su wadda a yanzu haka take kasa take dabo tun bayan martanin kungiyar Hamas.

Rahotanni dai sun ce tun tsakar dare mista Blinken ya farka daga barci yake ta nazarin sakon da Hamas ta mika wa Katar da Egypt masu shiga tsakani.

Kungiyar Hamas dai ta ce a shirye take ta yi maraba da yarjejeniyar to amma ta sa sharadin cewa sai idan Isra’ila ta amince da dakatar da yaki baki dayansa.

ADVERTISEMENT
  • Daga Karshe, Biden Ya Zamanto Irinsu Trump
  • Ba Za A Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gaza Ba Har Sai Amurka Ta Daina Samarwa Isra’ila Da Makamai

Gwamnatin Isra’ila dai ba ta mayar da martani ba amma kuma wani jami’in Isra’ilar wanda ba ya son a ambaci sunansa ya ce sauyin da Hamas ke son yi ga yarjejeniyar tamkar watsi da ita ne.

BBC na daga cikin tawagar ‘yan jaridar da ke tafiya da mista Blinken a ziyarar tasa zu-wa Birnin Doha inda yake ganawa da shugabannin Katar domin tabbatar da yarjejeni-yar ba ta samu cikas ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

A ranar Talata dai Mista Blinken da firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu sun kara nanata muhimmancin yarjejeniyar duk da cewa Mista Netanyahu bai fito fili ya yi maraba da yarjejeniyar ba wadda shugaban Amurka, Joe Biden ya ce Isra’ilar ce ta fito da ita.

Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Amurka, John Kirby ya ce ana duba martanin na Ha-mas. Kungiyar dai ta ce za ta hau teburin sulhu da zuciya daya.

“Mun karbi maratanin Hamas da ta gabatar ta hannun Katar da Egypt muna kuma nazartarsa yanzu haka kuma ina tunanin cewar iya abin da za mu iya yi kenan yanzu, tun da mun sami wannan martanin a hannun yanzu, kuma za mu yi aiki a kansa,” in ji Kirby.

Wakiliyar BBC ta ce wani jami’in Hamas Aze Tariksh ya ce martanin na su ya bude kofar cimma yarjrjeniya.

To amma wani jami’in Isra’ila da ya nemi a sakaye sunansa ya zargi Hamas da sauya wasu muhimman sassa na daftarin yarjejeniyar, kuma haka a wajensu, tamkar ta yi watsi da yarjejeniyar ne.

Jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya ta ce amincewa da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya yi, wani mataki ne na goyon bayan samar da zaman lafiya.

Linda Thomas-Greenfield ta ce kasashen duniya sun hada kai kan yarjejeniyar da za ta ceci rayuka, da mayar da mutanen Isra’ila da aka yi garkuwa da su gida da kuma taimaka wa fararen hula Falasdinawa.

A rubuce dai kudurin na nuna cewa Isra’ila ta amince da yarjejeniyar wadda shugaba Biden ya sanar a watan jiya.

Gaza
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya

Sallah: Tinubu Ya Bukaci Hadin Kai Da Sadaukarwa A Tsakanin 'Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

July 18, 2026
Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

July 18, 2026
Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

July 18, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

July 18, 2026
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

July 18, 2026
Xi Jinping Ya Bukaci A Gudanar Da Aikin Ceto A Tsanake Bayan Rugujewar Bangaren Wani Tsauni A Chongqing

Xi Jinping Ya Bukaci A Gudanar Da Aikin Ceto A Tsanake Bayan Rugujewar Bangaren Wani Tsauni A Chongqing

July 18, 2026
Yadda Ake Miyar Karkashi Da Nama

Yadda Ake Miyar Karkashi Da Nama

July 18, 2026
Kura-kurai 7 Da Mata Ke Yi Wajen Kula Da Fatarsu

Kura-kurai 7 Da Mata Ke Yi Wajen Kula Da Fatarsu

July 18, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 

Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

July 18, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.