ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawan Katsewar Network Na Haifar Mana Da Koma-baya A Harkar Kasuwanci – Masu POS

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Network

Masu sana’ar hada-hadar kudi na POS a Nijeriya sun koka kan yawaitar katsewar network din layukan waya daga kamfanonin sadarwa a Nijeriya inda suka misalta hakan a matsayin hanyoyin da ke janyo wa harkar kasuwancinsu koma baya.

Na’urar POS dai ya zama wani hanya mafi sauki da jama’a ke runguma wajen yin hada-hadar kudade kama daga shigar da kudadensu ko cirewa. Hakan kuma ya biyo bayan wahalar zuwa bankuna ko na’urar cirar kudi na ATM da jama’a ke fuskanta.

  • Amurka Na Dauke Da Nauyin Dakatar Da Kisan Fararen Hula A Rafah
  • Matsalar Tsaro A Nijeriya: Akwai Bukatar Daukar Kwakkwaran Mataki

A Nijeriya masu sana’ar POS wadanda mafi yawansu matasa ne sun kasance masu shiga tsakanin bankuna da kwastomomi inda suke saukaka wa bankuna matsalolin hulda da kudade.

ADVERTISEMENT

A ‘yan kwanakin nan an yi ta fuskanta matsalolin da suka shafi na katsewar network daga kamfanonin sadarwa, inda masu POS suka nuna hakan a matsayin babban matsala da ke kawo musu cikas.

Wani mai sana’ar POS a jihar Bauchi, Sulaiman Alhassan ya shaida wa shafin Kimiyya da fasaha cewa, “A ‘yan kwanakin nan muna fuskantar matsalolin network gaskiya. Har ta kai idan mutum na son kada ya rasa kwastomomi yadda yake so ko yadda ya saba to dole sai ya sayi data a layuka a kalla uku, idan wannan kamfanin ya katse sai ya canza zuwa wani kamfanin sadarwa, to matsalar da muke fuskanta ko a hakan ne ma, idan kwastoma ya zo kana kokarin canza layi zuwa wani domin ka samu karfin network din da za ka tura ko cire wa kwastoma kudi, a nan gabar sai hakurin mutum ya kare ka ga ya nemi wucewa zuwa wani wajen.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

“Na rasa kwastomomi sosai a irin wannan. Kuma dai daman cinikin ma ya ragu amma sakamakon matsalar network gaskiya muna rasa ciniki matuka.”

“Amma idan mutum ya dage yana da layuka da yawa kamar uku, duk da hakan ma asara muke yi, misali, idan zan sanya datar MTN na dubu uku na ci gaba da tura kudi ko cirewa, sai ya zama a kowani rana ina fargabar network zai iya dauke min, zan kuma sake wani datar dubu uku a zain ko glo ka ga ko ba komai na sake kashe wani kudin a wani abun da ban tsara yi ba.

“A zahiri yawaitar katsewar network na janyo mana cikas da matsaloli,” ya shaida.

Kazalika, wata mai sana’ar POS Mary Daniel daga jihar Gombe ta shaida cewar, “Layi daya nake amfani da shi, duk lokacin da network ya yanke sai dai na zauna na yi ta kallo. Babbar matsalar da muke fuskanta idan network din nan na yawa, za mu iya tura kudi ya zo bai je ba ko kuma ya fita bai nuna mana ba. Don haka a irin wannan fargabar kamar mu masu karamin karfi kawai na kan gwammace na hakura da cigaba da kasuwancin har sai an samu network mai karfi kafin na cigaba da yin kasuwancina. A hakan kuma asara kawai muke yi da bata lokaci,” ya shaida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

March 8, 2025
Next Post
Hedikwatar Tsaron Nijeriya Ta Bayyana Sunayen ‘Yan ta’adda 97 Da Ake Nema Ruwa A-jallo

Hedikwatar Tsaron Nijeriya Ta Bayyana Sunayen 'Yan ta'adda 97 Da Ake Nema Ruwa A-jallo

LABARAI MASU NASABA

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.