• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yobe Ta Arewa: APC Ta Sha Alwashin Daukaka Kara Kan Nasarar Machina A Kotu

by Sadiq
3 years ago
APC

Jam’iyyar APC reshen Jihar Yobe, ta sha alwashin daukaka kara kan hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Damaturu, Jihar Yobe, ta yanke wa Bashir Sheriff Machina, a matsayin wanda ya dace ya tsaya takarar Sanatan Yobe ta Arewa a zaben 2023. 

Jam’iyyar ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin duk da hukuncin da shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, wanda a halin yanzu ke kan kujerar Yobe ta Arewa a majalisar dokokin kasar, ya amince da hukuncin da kotun ta yanke.

  • Wadanne Abubuwa Ne Ake Iya Fasa Aure Saboda Su?
  • Matakan Farfado Da Masana’antun Fatu Na Haifar Da da Mai Ido A Nijeriya —Shugaban NILEST

Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Mohammed Gadaka, ya ce jam’iyyar ba ta amince da hukuncin ba.

Gadaka, a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, ya ce Lawan ya ci gaba da zama dan takarar jam’iyyar a zaben Yobe ta Arewa a 2023.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Muna sane da hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Damaturu, babban birnin Jihar Yobe ta yanke a ranar Laraba, 28 ga Satumba, 2022, game da zaben Sanatan Yobe ta Arewa da ke tafe.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Duk da haka, cikin girmamawa mun yi watsi da matakin da Shugaban Majalisar Dattawa, Mai Girma Sanata Ahmad Lawan ya dauka na amincewa da hukuncin da kotun ta yanke wanda ya haramta masa tsayawa takara da kuma shiga zaben.

“A bisa hakkinmu na shari’a, jam’iyyar APC reshen Jihar Yobe ta yanke shawarar daukaka kara kan hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke domin alfanun Jihar Yobe da Nijeriya da kuma shugabanci na gari, dole ne mu kare tare da dorewar Sanata Ahmed Lawan. -Shekaru asharin da uku wanda ya yi abin koyi a matsayin dan majalisa da kuma tarihinsa na shugabanci da kishin kasa – da kuma jajircewarsa na ganin Nijeriya ta yi aiki.”

Idan za a tunawa a ranar Larabar da ta gabata ne mai shari’a Fadima Murtala Aminu, ta babbar kotun tarayya da ke Damaturu a Jihar Yobe, ta ayyana Machina a matsayin dan takarar Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC.

Alkalin ta kuma umarci jam’iyyar APC da ta mika sunan Machina ga INEC a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani a Yobe ta Arewa.

Alkalin ta yi watsi da zargin zaben fidda gwani, inda shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya fito a matsayin dan takarar sanata a matsayin wanda ya lashe zaben.

Lawan wanda ya halarci zaben fidda gwanin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, daga bisani ya tafi neman tikitin takarar kujerar sanatan yankinsa, matakin da Machina ya kalubalanci shi, inda ya bayyana cewa ya shiga zaben fidda gwani na Jihar Yobe ta Arewa, kuma ya lashe zaben.

Da yake mayar da martani kan hukuncin kotun a wata sanarwa a ranar Alhamis, shugaban majalisar dattawan, ya ce ba zai daukaka kara kan hukuncin ba, kuma ya amince da Machina a matsayin wanda ya cancanta ya yi takarar Sanatan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Next Post
Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa: Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sa Ni Kuka 

Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa: Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sa Ni Kuka 

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.