• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yobe Ta Arewa: APC Ta Sha Alwashin Daukaka Kara Kan Nasarar Machina A Kotu

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
Yobe Ta Arewa: APC Ta Sha Alwashin Daukaka Kara Kan Nasarar Machina A Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC reshen Jihar Yobe, ta sha alwashin daukaka kara kan hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Damaturu, Jihar Yobe, ta yanke wa Bashir Sheriff Machina, a matsayin wanda ya dace ya tsaya takarar Sanatan Yobe ta Arewa a zaben 2023. 

Jam’iyyar ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin duk da hukuncin da shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, wanda a halin yanzu ke kan kujerar Yobe ta Arewa a majalisar dokokin kasar, ya amince da hukuncin da kotun ta yanke.

  • Wadanne Abubuwa Ne Ake Iya Fasa Aure Saboda Su?
  • Matakan Farfado Da Masana’antun Fatu Na Haifar Da da Mai Ido A Nijeriya —Shugaban NILEST

Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Mohammed Gadaka, ya ce jam’iyyar ba ta amince da hukuncin ba.

Gadaka, a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, ya ce Lawan ya ci gaba da zama dan takarar jam’iyyar a zaben Yobe ta Arewa a 2023.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Muna sane da hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Damaturu, babban birnin Jihar Yobe ta yanke a ranar Laraba, 28 ga Satumba, 2022, game da zaben Sanatan Yobe ta Arewa da ke tafe.

Labarai Masu Nasaba

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

“Duk da haka, cikin girmamawa mun yi watsi da matakin da Shugaban Majalisar Dattawa, Mai Girma Sanata Ahmad Lawan ya dauka na amincewa da hukuncin da kotun ta yanke wanda ya haramta masa tsayawa takara da kuma shiga zaben.

“A bisa hakkinmu na shari’a, jam’iyyar APC reshen Jihar Yobe ta yanke shawarar daukaka kara kan hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke domin alfanun Jihar Yobe da Nijeriya da kuma shugabanci na gari, dole ne mu kare tare da dorewar Sanata Ahmed Lawan. -Shekaru asharin da uku wanda ya yi abin koyi a matsayin dan majalisa da kuma tarihinsa na shugabanci da kishin kasa – da kuma jajircewarsa na ganin Nijeriya ta yi aiki.”

Idan za a tunawa a ranar Larabar da ta gabata ne mai shari’a Fadima Murtala Aminu, ta babbar kotun tarayya da ke Damaturu a Jihar Yobe, ta ayyana Machina a matsayin dan takarar Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC.

Alkalin ta kuma umarci jam’iyyar APC da ta mika sunan Machina ga INEC a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani a Yobe ta Arewa.

Alkalin ta yi watsi da zargin zaben fidda gwani, inda shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya fito a matsayin dan takarar sanata a matsayin wanda ya lashe zaben.

Lawan wanda ya halarci zaben fidda gwanin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, daga bisani ya tafi neman tikitin takarar kujerar sanatan yankinsa, matakin da Machina ya kalubalanci shi, inda ya bayyana cewa ya shiga zaben fidda gwani na Jihar Yobe ta Arewa, kuma ya lashe zaben.

Da yake mayar da martani kan hukuncin kotun a wata sanarwa a ranar Alhamis, shugaban majalisar dattawan, ya ce ba zai daukaka kara kan hukuncin ba, kuma ya amince da Machina a matsayin wanda ya cancanta ya yi takarar Sanatan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ahmad lawanAlkaliAPCHukuncin KotuKotuMachinaShugaban Majalisar DattawaYobe ta Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wadanne Abubuwa Ne Ake Iya Fasa Aure Saboda Su?

Next Post

Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa: Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sa Ni Kuka 

Related

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC
Siyasa

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

4 hours ago
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu
Siyasa

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

6 hours ago
Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami
Manyan Labarai

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

16 hours ago
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar
Siyasa

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

1 day ago
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

2 days ago
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
Manyan Labarai

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

2 days ago
Next Post
Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa: Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sa Ni Kuka 

Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa: Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sa Ni Kuka 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.