• Leadership Hausa
Thursday, September 21, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yobe Ta Arewa: APC Ta Sha Alwashin Daukaka Kara Kan Nasarar Machina A Kotu

by Sadiq
12 months ago
in Siyasa
0
Yobe Ta Arewa: APC Ta Sha Alwashin Daukaka Kara Kan Nasarar Machina A Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC reshen Jihar Yobe, ta sha alwashin daukaka kara kan hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Damaturu, Jihar Yobe, ta yanke wa Bashir Sheriff Machina, a matsayin wanda ya dace ya tsaya takarar Sanatan Yobe ta Arewa a zaben 2023. 

Jam’iyyar ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin duk da hukuncin da shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, wanda a halin yanzu ke kan kujerar Yobe ta Arewa a majalisar dokokin kasar, ya amince da hukuncin da kotun ta yanke.

  • Wadanne Abubuwa Ne Ake Iya Fasa Aure Saboda Su?
  • Matakan Farfado Da Masana’antun Fatu Na Haifar Da da Mai Ido A Nijeriya —Shugaban NILEST

Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Mohammed Gadaka, ya ce jam’iyyar ba ta amince da hukuncin ba.

Gadaka, a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, ya ce Lawan ya ci gaba da zama dan takarar jam’iyyar a zaben Yobe ta Arewa a 2023.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Muna sane da hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Damaturu, babban birnin Jihar Yobe ta yanke a ranar Laraba, 28 ga Satumba, 2022, game da zaben Sanatan Yobe ta Arewa da ke tafe.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

Kotun Sauraren Kararrakin Zabe Dan Majalisar Wakilai A Kano Ta Tabbatar Da Nasarar Kofa

“Duk da haka, cikin girmamawa mun yi watsi da matakin da Shugaban Majalisar Dattawa, Mai Girma Sanata Ahmad Lawan ya dauka na amincewa da hukuncin da kotun ta yanke wanda ya haramta masa tsayawa takara da kuma shiga zaben.

“A bisa hakkinmu na shari’a, jam’iyyar APC reshen Jihar Yobe ta yanke shawarar daukaka kara kan hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke domin alfanun Jihar Yobe da Nijeriya da kuma shugabanci na gari, dole ne mu kare tare da dorewar Sanata Ahmed Lawan. -Shekaru asharin da uku wanda ya yi abin koyi a matsayin dan majalisa da kuma tarihinsa na shugabanci da kishin kasa – da kuma jajircewarsa na ganin Nijeriya ta yi aiki.”

Idan za a tunawa a ranar Larabar da ta gabata ne mai shari’a Fadima Murtala Aminu, ta babbar kotun tarayya da ke Damaturu a Jihar Yobe, ta ayyana Machina a matsayin dan takarar Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC.

Alkalin ta kuma umarci jam’iyyar APC da ta mika sunan Machina ga INEC a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani a Yobe ta Arewa.

Alkalin ta yi watsi da zargin zaben fidda gwani, inda shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya fito a matsayin dan takarar sanata a matsayin wanda ya lashe zaben.

Lawan wanda ya halarci zaben fidda gwanin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, daga bisani ya tafi neman tikitin takarar kujerar sanatan yankinsa, matakin da Machina ya kalubalanci shi, inda ya bayyana cewa ya shiga zaben fidda gwani na Jihar Yobe ta Arewa, kuma ya lashe zaben.

Da yake mayar da martani kan hukuncin kotun a wata sanarwa a ranar Alhamis, shugaban majalisar dattawan, ya ce ba zai daukaka kara kan hukuncin ba, kuma ya amince da Machina a matsayin wanda ya cancanta ya yi takarar Sanatan.

Tags: Ahmad lawanAlkaliAPCHukuncin KotuKotuMachinaShugaban Majalisar DattawaYobe ta Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wadanne Abubuwa Ne Ake Iya Fasa Aure Saboda Su?

Next Post

Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa: Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sa Ni Kuka 

Related

Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi
Labarai

Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

5 hours ago
Kotun Sauraren Kararrakin Zabe Dan Majalisar Wakilai A Kano Ta Tabbatar Da Nasarar Kofa
Labarai

Kotun Sauraren Kararrakin Zabe Dan Majalisar Wakilai A Kano Ta Tabbatar Da Nasarar Kofa

2 weeks ago
Kotun Sauraren Kararrakin Zaben Sanata Ta Tsige Sanata Jibril Isah Na Mazabar Kogi Ta Gabas
Manyan Labarai

Kotun Sauraren Kararrakin Zaben Sanata Ta Tsige Sanata Jibril Isah Na Mazabar Kogi Ta Gabas

2 weeks ago
NNPP Ta Maka Kwankwaso A Kotu Kan Zargin Yi Wa Jam’iyya Makarkashiya
Manyan Labarai

DA DUMI DUMINSA: Kotu Ta Dakatar Da Korar Kwankwaso Daga Jam’iyyar NNPP

2 weeks ago
Dan Takarar Gwamnan Jam’iyyar NNPP A Jihar Benue Ya Fice Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Dan Takarar Gwamnan Jam’iyyar NNPP A Jihar Benue Ya Fice Daga Jam’iyyar

4 weeks ago
NNPP Ta Maka Kwankwaso A Kotu Kan Zargin Yi Wa Jam’iyya Makarkashiya
Manyan Labarai

NNPP Ta Maka Kwankwaso A Kotu Kan Zargin Yi Wa Jam’iyya Makarkashiya

1 month ago
Next Post
Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa: Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sa Ni Kuka 

Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa: Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sa Ni Kuka 

LABARAI MASU NASABA

Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sin Da Amurka Da Su Kyautata Matakan Shawo Kan Sabani

Han Zheng Ya Yi Kira Ga Sin Da Amurka Da Su Kyautata Matakan Shawo Kan Sabani

September 21, 2023
Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

Sin Da Kasashe Masu Ra’ayi Iri Daya Sun Yi Kira Da A Inganta Rayuwar Mata Masu Bukata Ta Musamman A Cikin Al’umma

September 21, 2023
Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba

Bai Dace Takara Ta Zamo Kalmar Kwatanta Alakar Sin Da Amurka Ba

September 21, 2023
Yawan Jarin Da Sin Ta Zuba A Ketare Daga Janairu Zuwa Agusta Ya Rika Karuwa

Yawan Jarin Da Sin Ta Zuba A Ketare Daga Janairu Zuwa Agusta Ya Rika Karuwa

September 21, 2023
Super Eagles Ta Nijeriya Ta Dawo Mataki Na 40 A Jadawalin Kasashen Da Suka Fi Iya Taka Leda A Duniya

Super Eagles Ta Nijeriya Ta Dawo Mataki Na 40 A Jadawalin Kasashen Da Suka Fi Iya Taka Leda A Duniya

September 21, 2023
Sin Ta Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kare Mabanbantan Halittun Teku

Sin Ta Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kare Mabanbantan Halittun Teku

September 21, 2023
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Zhejiang

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Zhejiang

September 21, 2023
Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Shaibu Ya Roki Obaseki Ya Gafarce Shi

September 21, 2023
IPC

IPC Ta Yi Tir Da Muzguna Wa ‘Yan Jarida Yayin Daukan Rahoton Shari’ar Kujerar Gwamna A Kano

September 21, 2023
Bayan Gindaya Wa’adi: Hukumar AGIS Na Tattara Harajin Naira Biliyan Daya A Kullum 

Bayan Gindaya Wa’adi: Hukumar AGIS Na Tattara Harajin Naira Biliyan Daya A Kullum 

September 21, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.