ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yobe Ta Arewa: APC Ta Sha Alwashin Daukaka Kara Kan Nasarar Machina A Kotu

by Sadiq
4 years ago
APC

Jam’iyyar APC reshen Jihar Yobe, ta sha alwashin daukaka kara kan hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Damaturu, Jihar Yobe, ta yanke wa Bashir Sheriff Machina, a matsayin wanda ya dace ya tsaya takarar Sanatan Yobe ta Arewa a zaben 2023. 

Jam’iyyar ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin duk da hukuncin da shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, wanda a halin yanzu ke kan kujerar Yobe ta Arewa a majalisar dokokin kasar, ya amince da hukuncin da kotun ta yanke.

  • Wadanne Abubuwa Ne Ake Iya Fasa Aure Saboda Su?
  • Matakan Farfado Da Masana’antun Fatu Na Haifar Da da Mai Ido A Nijeriya —Shugaban NILEST

Shugaban jam’iyyar APC na jihar, Mohammed Gadaka, ya ce jam’iyyar ba ta amince da hukuncin ba.

ADVERTISEMENT

Gadaka, a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, ya ce Lawan ya ci gaba da zama dan takarar jam’iyyar a zaben Yobe ta Arewa a 2023.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Muna sane da hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Damaturu, babban birnin Jihar Yobe ta yanke a ranar Laraba, 28 ga Satumba, 2022, game da zaben Sanatan Yobe ta Arewa da ke tafe.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

“Duk da haka, cikin girmamawa mun yi watsi da matakin da Shugaban Majalisar Dattawa, Mai Girma Sanata Ahmad Lawan ya dauka na amincewa da hukuncin da kotun ta yanke wanda ya haramta masa tsayawa takara da kuma shiga zaben.

“A bisa hakkinmu na shari’a, jam’iyyar APC reshen Jihar Yobe ta yanke shawarar daukaka kara kan hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke domin alfanun Jihar Yobe da Nijeriya da kuma shugabanci na gari, dole ne mu kare tare da dorewar Sanata Ahmed Lawan. -Shekaru asharin da uku wanda ya yi abin koyi a matsayin dan majalisa da kuma tarihinsa na shugabanci da kishin kasa – da kuma jajircewarsa na ganin Nijeriya ta yi aiki.”

Idan za a tunawa a ranar Larabar da ta gabata ne mai shari’a Fadima Murtala Aminu, ta babbar kotun tarayya da ke Damaturu a Jihar Yobe, ta ayyana Machina a matsayin dan takarar Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC.

Alkalin ta kuma umarci jam’iyyar APC da ta mika sunan Machina ga INEC a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani a Yobe ta Arewa.

Alkalin ta yi watsi da zargin zaben fidda gwani, inda shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya fito a matsayin dan takarar sanata a matsayin wanda ya lashe zaben.

Lawan wanda ya halarci zaben fidda gwanin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC kuma ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, daga bisani ya tafi neman tikitin takarar kujerar sanatan yankinsa, matakin da Machina ya kalubalanci shi, inda ya bayyana cewa ya shiga zaben fidda gwani na Jihar Yobe ta Arewa, kuma ya lashe zaben.

Da yake mayar da martani kan hukuncin kotun a wata sanarwa a ranar Alhamis, shugaban majalisar dattawan, ya ce ba zai daukaka kara kan hukuncin ba, kuma ya amince da Machina a matsayin wanda ya cancanta ya yi takarar Sanatan.

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa: Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sa Ni Kuka 

Kakakin Majalisar Dokokin Nasarawa: Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Sa Ni Kuka 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.