• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Haramta Amfani Da TikTok A Amurka

by Sadiq
1 year ago
in Kasashen Ketare
0
Za A Haramta Amfani Da TikTok A Amurka

LONDON, ENGLAND - FEBRUARY 28: In this photo illustration, a TikTok logo is displayed on an iPhone on February 28, 2023 in London, England. This week, the US government and European Union's parliament have announced bans on installing the popular social media app on staff devices. (Photo by Dan Kitwood/Getty Images)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar wakilan Amurka ta zartar da muhimmin kudirin da ka iya haramta amfani da manhajar Tiktok a kasar.

Dokar za ta bai wa katafaren kamfanin sada zumunta na “ByteDance” mallakin kasar China, wa’adin watanni shida ya sayar da hannayen jarinsa ko kuma a toshe manhajar a fadin Amurka.

  • Kasar Sin Na Kira Ga Amurka Ta Daina Danne Kamfanonin Waje Ba Bisa Adalci Ba
  • Ci Gaban Kasar Sin Na Ingiza Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya

‘Yan majalisar sun jima suna nuna damuwa game da tasirin kasar China a kan manhajar ta TikTok.

Kamfanin kasar China Bytedance ne ya mallaki manhajar ta TikTok da aka kirkira a shekarar 2012.

An yi wa kamfanin mai mazauni a birnin Beijing rijista ne, a tsibirin Cayman, amma yana da ofisoshi a fadin nahiyar Turai da Amurka.

Labarai Masu Nasaba

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Idan har kudirin bai samu sahalewar Majalisar Dattawan Amurka ba, Shugaba Joe Biden ya ce ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen rattaba masa hannu da zarar ya iso kan teburinsa, abin da ake ganin na iya sabbaba takaddamar diflomasiya da kasar China.

Kamfanin Bytedance na bukatar samun sahalewar jami’an kasar China kafin kammala cefanar da hannayen jarinsa, matakin da mahukuntan birnin Beijing suka sha alwashin kalubalanta.

Akwai dokar tsaron China da ta bukaci kamfanonin kasar su yi musayar bayanai da gwamnati matukar aka bukaci hakan.

Manhajar ta TikTok ta yi kokarin bai wa hukumomin da ke sanya idanu a kan shafukan sada zumunta tabbacin cewar ta dauki matakan kare bayanan mutum milyan 150 da ke amfani da ita a Amurka daga ma’aikatan kamfanin Bytedance da ke kasar China.

Duk da cewar majalisar na da mambobi daga jam’iyyu guda biyu, an zartar da kudirin da kyakkyawan rinjaye, amma duk da haka sai ya samu sahalewar majalisar dattawa da sa hannun shugaban kasar kafin ya zama doka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaChinaDokaMajalisar WakilaiTikTok
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Kira Ga Amurka Ta Daina Danne Kamfanonin Waje Ba Bisa Adalci Ba

Next Post

Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoto Mai Taken “’Yancin Fadin Albarkacin Baki A Amurka: Gaskiya Da Hujjoji”

Related

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine
Kasashen Ketare

Trump Ya Bai Wa Rasha Kwanaki 50 Ta Kawo Ƙarshen Yaƙinta Da Ukraine

16 hours ago
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari
Kasashen Ketare

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

1 day ago
Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
Kasashen Ketare

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

2 days ago
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka
Kasashen Ketare

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

3 days ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

3 days ago
Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan
Kasashen Ketare

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

1 week ago
Next Post
Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoto Mai Taken “’Yancin Fadin Albarkacin Baki A Amurka: Gaskiya Da Hujjoji”

Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoto Mai Taken “’Yancin Fadin Albarkacin Baki A Amurka: Gaskiya Da Hujjoji”

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.