• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Yi Dokar Hukunta Masu Kona Alkur’ani A Denmark

by Leadership Hausa
2 years ago
in Ra'ayoyi
0
Za A Yi Dokar Hukunta Masu Kona Alkur’ani A Denmark
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin kasar Denmark ta dauki aniyar haramta kona Alkur’ani Mai Tsarki a bainar jama’a bayan jerin kone-konen da suka haddasa yamutsi a kasashen Musulmai.

Ministan shari’ar kasar, Peter Hummelgaard ya ce irin wannan mataki na kona Alkur’ani ya cutar da Denmark kuma ya sanya al’ummarta cikin hatsari.

  • Gwamnan Kaduna Ya Bude Masaukin Dalibai Mai Gado 400 Da Ofishin Hukumar Raya Birnin Zariya
  • An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana’o’i A Kano

Dokar wadda ake shirin kafawa za ta mayar da duk wani matakin wulakanta Alkur’ani ko Littafin Bayabul, matsayin laifi da za a iya hukunta mutum, ta hanyar cin tara ko dauri a gidan yari tsawon shekara biyu ko sama da haka.

Gwamnatin kasar mai sassaucin ra’ayi ta ce tana son aika wani sako ga al’ummar duniya.

Ministan harkokin waje, Lars Lokke Rasmussen ya ce Denmark ta shaida jerin zanga-zanga har 170 cikin ‘yan makonnin nan, a ciki har da kona Kur’anai a gaban ofisoshin jakadancin ksashen waje.

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Hukumar leken asirin Denmark ta yi gargadin cewa al’amuran da suka faru a baya-bayan nan sun tsananta barazanar kai harin ta’addanci.

Ita ma kasar Sweden mai makwabtaka ta shaida jerin kone-konen Alkur’ani kuma jami’an tsaronta sun yi gargadin cewa al’amuran tsaro za su tabarbare. A watan Yuli, masu zanga-zanga sun cinna wuta kan ofishin jakadancinta a Iraki.

Sai dai duka kasashen Denmark da Sweden sun jinkirta daukar mataki a kan kone-konen saboda dokokinsu na sassaucin ra’ayi a kan ‘yancin fadar albarkacin baki.

A shekarun 1970 ne Sweden ta soke dokarta ta haramta sabo. Gwamnatin birnin Copenhagen ta yanke shawarar daukar mataki bayan karin kone-konen Alkur’ani a karshen watan Yuli cikin Denmark da Sweden.

Kungiyar Kasashen Musulmai ta Duniya (OIC) ta yi kira ga mambobinta su dauki matakan da suka dace a kan kasashen da ake wulakanta Alkur’ani.

Ministan shari’ar ya dage a kan cewa kudurin canza dokar ba zai shafi furuci ko rubutun bayyana albarkacin baki ko zanen shagube ba. Sai dai ya ce kona littattafan addinai ba su da wata manufa sai haifar da baraka da haddasa gaba.

“Wani ginshikin al’amari ne ga tsarin dimokradiyyarmu cewa mutum na da ‘yancin fadar albarkacin bakinsa,” a cewar Mataimakin firaminista Jakob Ellemann-Jensen. “Kuma ya kamata mutum ya rika sara, yana duban bakin gatari.”

Denmark ba za ta tsaya ta zuba ido kawai ba a lokacin da irin wadannan abubuwa masu nakasu ga tsaron kasar ke faruwa, ya kara da cewa.

Firaministan Sweden, Ulf Kristersson, ya ce gwamnatin Stockholm ba za ta dauki irin wannan mataki na makwabciyarta ba, saboda hakan mai yiwuwa zai bukaci yi wa tsarin mulkin kasar garambawul.

Ministan shari’ar Sweden Gunnar Strommer ya fada wa manema labarai cewa shawarar sake nazari kan dokar tabbatar da kwanciyar hankalin jama’a, ta yi daidai.

Gwamnatin kasar na son canza dokar domin ta haramta tarukan da za su yi barazana ga tsaron al’ummar Sweden.

Ministoci a Denmark sun kuduri aniyar yi wa dokar sauye-sauye ranar 1 ga watan Satumba, sannan su gabatar da sauye-sauyen ga majalisar dokoki don zatarwa kafin karshen wannan shekara.

Ana sa ran, haramcin za a yi shi ne a sashen kundin aikata laifuka da ke hana ‘yan kasar muzanta wata kasar waje, ko tutarta da sauran wani tambarinta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Aikin Titin Da Zai Hade Kauyuka 32 A Ikara Da Kubau

Next Post

Gwamnatin Sokoto Za Ta Kashe Biliyan 20.3 Domin Sayen Abinci Da Wasu Ayyuka

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

6 months ago
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

10 months ago
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

11 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

11 months ago
BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

BuÉ—aÉ—É—iyar WasiÆ™a Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

11 months ago
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Ra'ayoyi

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

1 year ago
Next Post
Gwamnatin Sokoto Za Ta Kashe Biliyan 20.3 Domin Sayen Abinci Da Wasu Ayyuka

Gwamnatin Sokoto Za Ta Kashe Biliyan 20.3 Domin Sayen Abinci Da Wasu Ayyuka

LABARAI MASU NASABA

Mun KaÉ—u MatuÆ™a Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

September 8, 2025
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

September 8, 2025
DSS Ta Ba Sowore Mako ÆŠaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

DSS Ta Ba Sowore Mako ÆŠaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

September 8, 2025
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

September 8, 2025
Kwamitin JAMB Ya BankaÉ—o Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Kwamitin JAMB Ya BankaÉ—o Magudin Jarabawa A 2025 UTME

September 8, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin GargaÉ—i Na Mako ÆŠaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin GargaÉ—i Na Mako ÆŠaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.