ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Yi Dokar Hukunta Masu Kona Alkur’ani A Denmark

by Leadership Hausa
2 years ago
AlKur'ani

Gwamnatin kasar Denmark ta dauki aniyar haramta kona Alkur’ani Mai Tsarki a bainar jama’a bayan jerin kone-konen da suka haddasa yamutsi a kasashen Musulmai.

Ministan shari’ar kasar, Peter Hummelgaard ya ce irin wannan mataki na kona Alkur’ani ya cutar da Denmark kuma ya sanya al’ummarta cikin hatsari.

  • Gwamnan Kaduna Ya Bude Masaukin Dalibai Mai Gado 400 Da Ofishin Hukumar Raya Birnin Zariya
  • An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana’o’i A Kano

Dokar wadda ake shirin kafawa za ta mayar da duk wani matakin wulakanta Alkur’ani ko Littafin Bayabul, matsayin laifi da za a iya hukunta mutum, ta hanyar cin tara ko dauri a gidan yari tsawon shekara biyu ko sama da haka.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin kasar mai sassaucin ra’ayi ta ce tana son aika wani sako ga al’ummar duniya.

Ministan harkokin waje, Lars Lokke Rasmussen ya ce Denmark ta shaida jerin zanga-zanga har 170 cikin ‘yan makonnin nan, a ciki har da kona Kur’anai a gaban ofisoshin jakadancin ksashen waje.

LABARAI MASU NASABA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

Hukumar leken asirin Denmark ta yi gargadin cewa al’amuran da suka faru a baya-bayan nan sun tsananta barazanar kai harin ta’addanci.

Ita ma kasar Sweden mai makwabtaka ta shaida jerin kone-konen Alkur’ani kuma jami’an tsaronta sun yi gargadin cewa al’amuran tsaro za su tabarbare. A watan Yuli, masu zanga-zanga sun cinna wuta kan ofishin jakadancinta a Iraki.

Sai dai duka kasashen Denmark da Sweden sun jinkirta daukar mataki a kan kone-konen saboda dokokinsu na sassaucin ra’ayi a kan ‘yancin fadar albarkacin baki.

A shekarun 1970 ne Sweden ta soke dokarta ta haramta sabo. Gwamnatin birnin Copenhagen ta yanke shawarar daukar mataki bayan karin kone-konen Alkur’ani a karshen watan Yuli cikin Denmark da Sweden.

Kungiyar Kasashen Musulmai ta Duniya (OIC) ta yi kira ga mambobinta su dauki matakan da suka dace a kan kasashen da ake wulakanta Alkur’ani.

Ministan shari’ar ya dage a kan cewa kudurin canza dokar ba zai shafi furuci ko rubutun bayyana albarkacin baki ko zanen shagube ba. Sai dai ya ce kona littattafan addinai ba su da wata manufa sai haifar da baraka da haddasa gaba.

“Wani ginshikin al’amari ne ga tsarin dimokradiyyarmu cewa mutum na da ‘yancin fadar albarkacin bakinsa,” a cewar Mataimakin firaminista Jakob Ellemann-Jensen. “Kuma ya kamata mutum ya rika sara, yana duban bakin gatari.”

Denmark ba za ta tsaya ta zuba ido kawai ba a lokacin da irin wadannan abubuwa masu nakasu ga tsaron kasar ke faruwa, ya kara da cewa.

Firaministan Sweden, Ulf Kristersson, ya ce gwamnatin Stockholm ba za ta dauki irin wannan mataki na makwabciyarta ba, saboda hakan mai yiwuwa zai bukaci yi wa tsarin mulkin kasar garambawul.

Ministan shari’ar Sweden Gunnar Strommer ya fada wa manema labarai cewa shawarar sake nazari kan dokar tabbatar da kwanciyar hankalin jama’a, ta yi daidai.

Gwamnatin kasar na son canza dokar domin ta haramta tarukan da za su yi barazana ga tsaron al’ummar Sweden.

Ministoci a Denmark sun kuduri aniyar yi wa dokar sauye-sauye ranar 1 ga watan Satumba, sannan su gabatar da sauye-sauyen ga majalisar dokoki don zatarwa kafin karshen wannan shekara.

Ana sa ran, haramcin za a yi shi ne a sashen kundin aikata laifuka da ke hana ‘yan kasar muzanta wata kasar waje, ko tutarta da sauran wani tambarinta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

October 5, 2024
Next Post
Gwamnatin Sokoto Za Ta Kashe Biliyan 20.3 Domin Sayen Abinci Da Wasu Ayyuka

Gwamnatin Sokoto Za Ta Kashe Biliyan 20.3 Domin Sayen Abinci Da Wasu Ayyuka

LABARAI MASU NASABA

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.