ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Yi Dokar Hukunta Masu Kona Alkur’ani A Denmark

by Leadership Hausa
3 years ago
AlKur'ani

Gwamnatin kasar Denmark ta dauki aniyar haramta kona Alkur’ani Mai Tsarki a bainar jama’a bayan jerin kone-konen da suka haddasa yamutsi a kasashen Musulmai.

Ministan shari’ar kasar, Peter Hummelgaard ya ce irin wannan mataki na kona Alkur’ani ya cutar da Denmark kuma ya sanya al’ummarta cikin hatsari.

  • Gwamnan Kaduna Ya Bude Masaukin Dalibai Mai Gado 400 Da Ofishin Hukumar Raya Birnin Zariya
  • An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana’o’i A Kano

Dokar wadda ake shirin kafawa za ta mayar da duk wani matakin wulakanta Alkur’ani ko Littafin Bayabul, matsayin laifi da za a iya hukunta mutum, ta hanyar cin tara ko dauri a gidan yari tsawon shekara biyu ko sama da haka.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin kasar mai sassaucin ra’ayi ta ce tana son aika wani sako ga al’ummar duniya.

Ministan harkokin waje, Lars Lokke Rasmussen ya ce Denmark ta shaida jerin zanga-zanga har 170 cikin ‘yan makonnin nan, a ciki har da kona Kur’anai a gaban ofisoshin jakadancin ksashen waje.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Hukumar leken asirin Denmark ta yi gargadin cewa al’amuran da suka faru a baya-bayan nan sun tsananta barazanar kai harin ta’addanci.

Ita ma kasar Sweden mai makwabtaka ta shaida jerin kone-konen Alkur’ani kuma jami’an tsaronta sun yi gargadin cewa al’amuran tsaro za su tabarbare. A watan Yuli, masu zanga-zanga sun cinna wuta kan ofishin jakadancinta a Iraki.

Sai dai duka kasashen Denmark da Sweden sun jinkirta daukar mataki a kan kone-konen saboda dokokinsu na sassaucin ra’ayi a kan ‘yancin fadar albarkacin baki.

A shekarun 1970 ne Sweden ta soke dokarta ta haramta sabo. Gwamnatin birnin Copenhagen ta yanke shawarar daukar mataki bayan karin kone-konen Alkur’ani a karshen watan Yuli cikin Denmark da Sweden.

Kungiyar Kasashen Musulmai ta Duniya (OIC) ta yi kira ga mambobinta su dauki matakan da suka dace a kan kasashen da ake wulakanta Alkur’ani.

Ministan shari’ar ya dage a kan cewa kudurin canza dokar ba zai shafi furuci ko rubutun bayyana albarkacin baki ko zanen shagube ba. Sai dai ya ce kona littattafan addinai ba su da wata manufa sai haifar da baraka da haddasa gaba.

“Wani ginshikin al’amari ne ga tsarin dimokradiyyarmu cewa mutum na da ‘yancin fadar albarkacin bakinsa,” a cewar Mataimakin firaminista Jakob Ellemann-Jensen. “Kuma ya kamata mutum ya rika sara, yana duban bakin gatari.”

Denmark ba za ta tsaya ta zuba ido kawai ba a lokacin da irin wadannan abubuwa masu nakasu ga tsaron kasar ke faruwa, ya kara da cewa.

Firaministan Sweden, Ulf Kristersson, ya ce gwamnatin Stockholm ba za ta dauki irin wannan mataki na makwabciyarta ba, saboda hakan mai yiwuwa zai bukaci yi wa tsarin mulkin kasar garambawul.

Ministan shari’ar Sweden Gunnar Strommer ya fada wa manema labarai cewa shawarar sake nazari kan dokar tabbatar da kwanciyar hankalin jama’a, ta yi daidai.

Gwamnatin kasar na son canza dokar domin ta haramta tarukan da za su yi barazana ga tsaron al’ummar Sweden.

Ministoci a Denmark sun kuduri aniyar yi wa dokar sauye-sauye ranar 1 ga watan Satumba, sannan su gabatar da sauye-sauyen ga majalisar dokoki don zatarwa kafin karshen wannan shekara.

Ana sa ran, haramcin za a yi shi ne a sashen kundin aikata laifuka da ke hana ‘yan kasar muzanta wata kasar waje, ko tutarta da sauran wani tambarinta.

AlKur'ani
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
Gwamnatin Sokoto Za Ta Kashe Biliyan 20.3 Domin Sayen Abinci Da Wasu Ayyuka

Gwamnatin Sokoto Za Ta Kashe Biliyan 20.3 Domin Sayen Abinci Da Wasu Ayyuka

LABARAI MASU NASABA

Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

July 5, 2026
Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.