• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ceto Mutanen Da Aka Sace A Zamfara —’Yan Sanda

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Za Mu Ceto Mutanen Da Aka Sace A Zamfara —’Yan Sanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Zamfara, Kolo Yusuf, ya tura karin tawagar jami’an’yan sanda don ceto mata da kananan yara da ‘yan bindiga suka sace kwanan nan.

A cewarsa, wasu ‘yan bindiga da suka gudu ta hanyar Kucheri-Wanzamai-Gidan Chida a karamar hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara sun yi garkuwa da mata da yara a yankin.

  • Allah Ta’ala Ya Alakanta Azumi Da Kansa (SWT)•Yadda Azumin Ya Dara Sauran Ibadu
  • Allah Ya Yi Wa Mai Dakin Aminu Dantata, Hajiya Rabi Rasuwa

Leadership Hausa ta samu cewa wasu gungun ‘yan bindiga da suka tsere daga Jihar Zamfara sun yi awon gaba da dimbin jama’a daga kauyuka uku na Wanzamai, Gidan Chida da Kucheri. Galibin wadanda aka yi garkuwa da su kananan yara ne da ke aiki a gonakinsu a kauyukansu. Wasu daga cikinsu sun fito ne daga al’ummar Yankara da ke karamar hukumar Faskari a Jihar Katsina.

Leadership Hausa ta kuma samu labarin cewa kwanaki kadan kafin wannan aika-aikar da aka yi garkuwa da jama’a, wata tawagar jami’an soji ta kashe wasu ‘yan bindiga guda hudu da ake zargin ‘yan bindiga ne a wani samame da suka kai a unguwar Gidan Damo da ke karamar hukumar Tsafe.

A cewar wata majiya ta kusa da rundunar sojin, dakarun Operation Hadarin Daji sun kaddamar da hare-haren ba-zata a dajin Rugu tare da fatattakar ‘yan bindiga da dama inda suka tilasta musu barin matsuguninsu. An ba da rahoton cewa, ‘yan bindiga da dama sun samu raunuka daban-daban.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan Jihar Zamfara ta fitar mai dauke da sa hannun kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Muhammad Shehu, ta bukaci mazauna jihar da su yi watsi da wannan munanan kalamai da ake yadawa a wasu sassan kafafen yada labarai.

Rundunar ‘yan sandan ta kara tabbatar wa jama’a musamman iyalan wadanda aka yi garkuwa da su, cewa tana aiki tare da hadin gwiwar sojoji da ’yan banga domin kubutar da wadanda lamarin ya shafa tare da hada su da iyalansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SandaCetoGarkuwaHariSataYaraZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Na Neman Miliyan 30 Kudin Fansar Yaran Da Suka Sace A Zamfara

Next Post

Kungiyoyin Arewa Sun Yi Fatali Da Bukatar Sakin Nnamdi Kanu

Related

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

2 hours ago
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
Manyan Labarai

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

2 hours ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

12 hours ago
Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa
Manyan Labarai

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

18 hours ago
Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32
Manyan Labarai

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

19 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

1 day ago
Next Post
Kungiyoyin Arewa Sun Yi Fatali Da Bukatar Sakin Nnamdi Kanu

Kungiyoyin Arewa Sun Yi Fatali Da Bukatar Sakin Nnamdi Kanu

LABARAI MASU NASABA

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.