• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ko Takarar Gwamnan Kano Ta Yi Wa Sadiq Aminu Wali Girma?

by Buhari Abba Rano
3 years ago
Kano

Yayin da ake kara kusantar zabe a Nijeriya, jam’iyyun siyasa da wadanda su ka fito takara a mukamai na ci gaba da yada manufa tare da bayyana irin kyawawan manufofin da suke burin aiwatarwa, idan sun kai ga nasara a zaben shekarar 2023 da ke tafe.

A Jihar Kano, da ta zama cibiyar siyasar Nijeriya, akwai masu neman kujerar gwamna a jam’iyyu daban-daban kuma ake jin duriyarsu da kuma bayyana wa Kanawan irin tanadin da suka yi musu idan su ka kai ga nasara.

  • Gobara Ta Kone Shaguna 15 Da Lalata Kaya Na Miliyan 19 A Jihar Kwara
  • Gobara Ta Yi Barna A Kasuwar Sayar Da Kayan Masarufi Ta Singa Da Ke Kano.

Jami’yyar APC ce ke mulkin Jihar Kano, inda suke da Dakta Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin dan takara, sai kuma jami’yyar NNPP ta tsohon gwamna Rabi’u Kwankwaso da suke da Abba Kabiru Yusuf da kuma jami’yyar PDP da suke da Sadiq Aminu Bashir Wali a matsayin wanda zai yi wa jam’iyyar takara a 2023.

Wali, wanda tsohon Kwamishinan albarkatun ruwa ne a gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje, ya zama dan takarar gwamnan ne a jam’iyyar PDP bayan da ya yi nasara a zaben fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar.

Tun da farko jam’iyyar PDP a Kano ta fuskantar rikici a kan wane ne halastaccen dan takarar gwamnan a jami’yyar.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Muhammad Abacha da Sadiq Aminu Wali kowane a cikinsu na jin shi ne halastaccen dan takarar jam’iyyar, biyo bayan rikicin zaben fidda gwani da kowanne bangare ya gudanar karkashin sa idon hukumar zabe ta kasa INEC.

Shugabancin jam’iyya bangaren Shehu Wada Sagagi, ya gabatar da zaben fidda gwani na jam’iyyar kuma a matsayarsa, Muhammed Abacha ne ya samu nasara.

Bayan zuwa kotu da aka yi, kotu ta sake ayyana Sadiq Wali a matsayin halastaccen dan takarar da zai yi wa PDP takarar gwamna a Kano.

Sai dai duk da wannan damar da Wali din ya samu amma har yanzu ya gaza fitowa fili ya bayyana wa Kanawa manufofinsa da kuma irin tanadin da gwamnatinsu ta yi musu idan ya kai ga nasara.

Haka kuma wani abin mamaki ga lamarin Sadiq Aminu Wali, shi ne yadda ya ke biris da gayyatar da manyan kungiyoyi ke shirya wa ‘yan takarar gwamna a Kano, inda al’umma suke kallon ko bai shiryawa takarar ba.

Haka zalika, ko a lokacin da Sadiq Wali din ya ke Kwamishinan ruwa na Kano, babu wani abin a zo a gani da ya tabuka domin sai da ta kai ga yara ‘yan makaranta ba sa samun zuwa makaranta ko kuma ba sa zuwa da wuri sakamakon fadi-tashin neman ruwa.

Masu sharhi a kan al’amuran siyasar Kano da sauran ‘yan siyasar jihar, sun dade da bayyana Sadiq Aminu Wali, a matsayin dan gatan da bai san wanne hali talaka a Jihar Kano ke ciki ba, kuma ba shi da wani kuduri ko manufa da zai ciyar da Kano gaba idan ya zama gwamna a 2023.

Mafi yawan al’ummar Jihar Kano na kallon Sadiq Aminu Wali a matsayin “Sabon Yankan Rake” a siyasa domin ba shi da wata kwarewa ko gogewar da zai ja ragamar shugabancin Jihar Kano da ke da sama da mutum miliyan tara.

Kuma shi ma ya tabbatar wa da duniya hakan la’akari da yadda ya gaza fitowa fili ya tallata takararsa da manufofinsa ga Kanawa.

Babu shakka ya zama wajibi ga al’ummar Jihar Kano da su zabi jajirtaccen mutumin da ya ke da ilimin addinin Islama da kuma na zamani tare da gogewar aiki da kuma manufa wanda ya ke da sanayya tsakanin manyan ‘yan kasuwa da ‘yan boko da ma’aikatan gwamnati da kuma goyon bayan kungiyoyin fararen hula, ba wai su bi rububi wajen zabar “Yankan Rake” ko dan gatan da bai san daga ina zai fara magance matsalolin da su ka yi wa jihar katutu ba.

Buhari Abba dan jarida ne ya rubuto daga Kano, Najeriya

[email protected]

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Ambaliyar Ruwa A Jihar Bayelsa Kalubale Ne Mai Girman Gaske – Majalisar Dinkin Duniya

Yawan Adadin Mutane A Fadin Duniya Ya Doshi Mutum Biliyan 8 — MDD

LABARAI MASU NASABA

Kano

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.