• Leadership Hausa
Sunday, June 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Sarkin Musulmi Ya Nesanta Kansa Da Mara Wa Peter Obi Baya

Tawagar Yada Labaransa Sun Yi Allah Wadai Da Kokarin Shigar Da Sarkin Cikin Siyasa

by Khalid Idris Doya
4 months ago
in Manyan Labarai
0
2023: Sarkin Musulmi Ya Nesanta Kansa Da Mara Wa Peter Obi Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sarkin Musulmi, Sultan Sa’ad Abubakar III, ya karyata rahotonin da ke cewa ya mara wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi baya a zaben da ke tafe.

Wannan na cikin sanarwar da, Bashir Adefaka ya fitar a ranar Juma’a, insa ya karyata rahoton.

  • Bukatar Daukar Mataki Kan Kisan Da ‘Yansanda Ke Wa Fararen Hula
  • NIS Reshen Bayelsa Ta Fara Horar Da Jami’anta Kan Tsarin Aiki Da Sarrafa Makamai

Sanarwar ta ce, kwata-kwata irin wannan maganar ma ba za ta fito daga bakin Sarkin ba.

Idan za a tuna dai a ranar Alhamis ne wasu labarai suka karade kafafen sada zumunta cewa Sarkin Musulmi, ya ayyana goyon bayansa ga Peter Obi.

Sai dai a martanin da fadar Sarkin ta fitar, ta nesanta Sarkin daga wannan labari.

Labarai Masu Nasaba

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

“A zahirin gaskiya wannan labarin bai cancanci martaninmu ba, amma kawai don a fayyace komai shi ya sa muke cewa hankali ma ba zai kama wannan batun ba. A matsayinsa na Sarkin Musulmai, Shugaban Majalisar koli na Addinin Musulunci ba zai taba yin irin wannan maganganun ba, don haka jama’a da dama suka sha mamaki tare da shure labarin tun kafin a ce musu karya ce.

“Kuma yana da kyau al’ummar Nijeriya su gane cewa dan takarar LP, Peter Obi gaba daya ma bai ziyarci fadar Sultan a tsakanin ranakun Laraba da Alhamis ba. Ta yaya har zai furta irin wannan maganganun, hankali ma ba zai kama ba.

“Mun kalubanci masu yada wannan batun da cewa su fito da faifayin bidiyo ko sautin murya na Sultan da ke mara wa Peter Obi baya tare da watsi da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu kamar yadda suka nakalto a labarin karyarsu.

Idan ba haka ba, ya kamata su kauce wa shigar da sunan Sultan cikin hidimar siyasa domin wanke sunansa.”

Sanarwar ta ce masu wannan kamfen din ba za su iya karkatar da hankalin Sultan daga ci gaba da gudanar da kyawawan ayyukan da ya ke yi a matsayinsa na Sarkin Musulmi ba.

Tags: APCGoyon BayaLabaran KaryaLPPeter ObiSakkwatoSarkin MusulmiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Daukar Mataki Kan Kisan Da ‘Yansanda Ke Wa Fararen Hula

Next Post

Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro

Related

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano
Manyan Labarai

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

5 hours ago
Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu
Manyan Labarai

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

11 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

1 day ago
Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano
Manyan Labarai

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

1 day ago
Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

2 days ago
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur
Manyan Labarai

Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

2 days ago
Next Post
Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro

Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

June 4, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

June 4, 2023
Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

June 4, 2023
Sana’ar Kwalliya

Sana’ar Kwalliya

June 4, 2023
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

June 4, 2023
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

June 4, 2023
Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

June 4, 2023
Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

June 4, 2023
Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

June 4, 2023
Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

June 4, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.