• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: A Kasar Da Babu Manufa Kadai Kwankwaso Zai Iya Zama Shugaban Kasa – APC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
Kwankwaso

Shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Kano sun bayyana cewa a kasar da babu manufa ce kadai, jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso zai iya zama shugaban kasa. Sun kara da cewa NNPP za ta sha wahala wajen sake neman a zabenta a Jihar Kano a 2027 ba kamar yadda suke ikirarin cewa, Shugaban kasa Bola Tinubu ne zai wahala ba.

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas, ya bayyana cewa a yanzu haka jam’iyyarsu ta kara samun hadin kai tare da dinke barakar da suka samu a zaben da ya gabata kuma sun shirya tsaf wajen kayar da NNPP a Jihar Kano.

  • Jagororin Siyasar Arewa Raunana Ne Kuma A Rarrabe Suke – Salihu Lukman
  • Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa

Jigon APC ya ce sabanin rahoton da kafafen yada labarai suka bayar ga shugaban NNPP na Jihar Kano, Hashimu Dungurawa, jam’iyyar da ke mulkin jihar da jagoranta na kasa, Rabi’u Musa Kwankwaso ne za su fuskanci mummunar matsala kan rikicin masarautar Jihar Kano.

Shugaban jam’iyyar NNPP na Kano ya ce rikicin sarautar Jihar Kano na iya yin illa ga burin Shugaba Bola Tinubu wajen ci gba da mulki a karo na biyu a 2027.

Sai dai a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano ya ce ikirarin da shugaban jam’iyyar NNPP, Dungurawa ya yi alama ce da ke nuna gazawar jam’iyyar a jihar da kuma kasa baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Abbas ya kara da cewa abun kunya ne ya bayyana haka ganin irin rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar NNPP da kuma jagoranta, Kwankwaso, abin kunya ne ya yi ikirarin sake lashe zabe a 2027.

“An ce Kwankwaso ya samu kuri’u 1,454,649 a zaben 2023, wanda ke wakiltar kashi 6.23 ne kawai, kuma yawancinsu daga Kano ne ya samu kuri’un. Amma binciken da kafafen yada labarai suka yi bayan zaben ya nuna cewa Kwankwaso bai samu kuri’u 100,000 a wata jiha ban da Kano.”

Abbas ya yi nuni da cewa Kwankwaso ya samu kuri’u miliyan 1.2 ko kashi 19 cikin 100 na kuri’un da aka kada a yankin arewa maso yamma a yankinsa, kuma kusan bai samu komai ba a sauran yankunan kasar nan.

“Ta yaya za a yi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi daga kudu maso gabas ya yi wa Kwankwaso fintinkau a jihohi 13 na arewa kamar Kaduna, Taraba, Borno, Gombe, Kebbi, Kogi, Kwara, Neja, Sakkwato, Nasarawa, Filato, Adamawa da kuma Benuwai,” in ji shi.

Shugaban jam’iyyar APC ya ce al’ummar Kano da masu tunani a arewacin Nijeriya sun fahimci cewa, abin da gwamnatin tarayya ke bukata a rikicin masarautar Kano shi ne, ta tabbatar da doka da oda domin a samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin al’umma jihar.

A cewarsa, a zaben 2027, al’ummar Jihar Kano wadanda aka rusa gidajensu ba za su manta ba, al’ummar Jihar Kano wadanda aka lalata musu hanyoyin samun tattalin arziki da kasuwanci ba za su sake zaben NNPP ba. Mutanen da dama gwamnatin Jihar Kano ta daidaita.

Shugaban APC na Jihar Kano ya bayyana cewa batun zaben shugaban kasa a 2027 da shugaban jam’iyyar NNPP na Kano ya yi barazanar za su kayar da su a Kano manuniya ce ga gazawar gwamnatinsu, sannan kuma za su yi amfani da dukiyar al’ummar Jihar Kano wajen tallata Kwankwaso wanda ba zai iya zama shugaban kasa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Kamfanin Sin Ya Fara Gina Hanyar Motoci Masu Saurin Tafiya Ta Farko A Cote Di’voire

Kamfanin Sin Ya Fara Gina Hanyar Motoci Masu Saurin Tafiya Ta Farko A Cote Di’voire

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.