• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Majar Atiku Da Obi Da Kwankwaso Ta Fada Shakku

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Majar

Akwai alamun da ke nuna cewa tattaunawar maja a tsakanin Atiku Abubakar, Peter Obi, da kuma Rabiu Kwankwaso ta cika da shakku game da yiwuwarta.

Shakkun dai ya dabaibaye majan ne tun lokacin daKwankwaso, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya bayyana cewa shi ne zai lashe zaben shugaban kasa a 2027.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Rahotanni sun nuna cewa jagorar jam’iyyar NNPP ya yi wannan furuci ne a lokacin da ya kaddamar da sakatariyar jam’iyyar a Jihar Katsina kwanan nan.

Tsohon gwamnan Jihar Kano, wanda Atiku da Obi suka yi zawarcinsa, ya ci gaba da cewa jam’iyyarsa ta NNPP a shirye take ta karbi ragamar shugabancin kasa, jihohi da sauran mukamai a fadin Nijeriya a zaben 2027.

Baya ga sanarwar tasa, Kwankwaso ya yi ikirarin cewa jam’iyyar PDP ta riga ta mutu, kuma ta fita daga kan layi.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

“Ina so in tunatar da ku cewa jam’iyyar PDP ta riga ta mutu, saboda da muna cikin jam’iyyar, tun da suka fita daga kan layi, muka yanke shawarar barin jam’iyyar,” in ji shi.

Kafin kalamun na Kwankwaso, jam’iyyar PDP ta bayyana cewa manyan jiga-jigan ‘yan adawa na neman hadaka domin kalubalantar APC a zab0en 2027.

Mataimakin sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na asa, Ibrahim Abdullahi, ne ya bayyana haka a lokacin da yake tattaunawa a gidan talabijin na Channels.

Abdullahi ya tabbatar da cewa Atiku, Obi, da Kwankwaso suna tattaunawa kan yiwuwar yin kawance.

Ya koka da yadda jam’iyyar ta yi asarar kuri’u sama da miliyan daya, inda ya kara da cewa da Kwankwaso ko Obi sun ci gaba da zama a jam’iyyar, “da mun rufe gibi da kuma kauce wa matsalolin siyasa da tattalin arziki da ake ciki a yanzu.

“Tabbas. Ana ci gaba da tattaunawa. Kun ga Peter Obi yana tattaunawa da Atiku. Kun ga Peter Obi yana ganawa da el-Rufai,” inji Abdullahi, inda ya kara da cewa jam’iyyarsu na kokarin ganin Obi, Kwankwaso, da sauran shugabannin da suka bar PDP sun jam’iyyar kafin zaben 2027.

“Daya daga cikinsu zai yarda da sauran, sannan za mu sami alkibla. Damuwarmu a matsayin jam’iyya da kuma wadannan mutanen da na ambata shi ne za su ceto ‘yan Nijeriya daga irin wannan kunci da yunwa da fatara da rashin tsaro da ke damun kasar nan,” ya kara shaidawa.

Idan za a iya tuna kafin zaben 2023, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku, a wata hira da BBC, ya yi nuni da cewa akwai yiwuwar kawance da Obi da Kwankwaso, amma hakan bai faruwa ba.

Bugu da kari, an kuma samu rashin nasara a tattaunawar da aka yi kan kawance tsakanin Peter Obi na jam’iyyar LP da Rabiu Kwankwaso na NNPP, a daya bangaren.

Da yake magana a wata hira da ya yi da gidan talabijin na News Central, Obi ya ce ba ya neman shugabancin Nijeriya ta kowacce hanya.

Ya ce zai amince a yi aiki tare da wasu ne kawai idan ya ga mutanen da za su iya yin aikin da kyau.

A cewarsa, ba zai hada kai da kowa ba don manufar kama jihar ko kuma ya ci zabe.

Masana harkokin siyasa na nuna shakku kan kawancin Atiku da Kwankwaso da kuma Obi wajen kawar da jam’iyyar APC daga kan karagar mulkin Nijeriya. Wanda suke ganin kamar an samu matsala duba da irin kalamun da Kwankwaso ya furta da kuma irin martanin da PDP ta mayar masa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.