ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Majar Atiku Da Obi Da Kwankwaso Ta Fada Shakku

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Majar

Akwai alamun da ke nuna cewa tattaunawar maja a tsakanin Atiku Abubakar, Peter Obi, da kuma Rabiu Kwankwaso ta cika da shakku game da yiwuwarta.

Shakkun dai ya dabaibaye majan ne tun lokacin daKwankwaso, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya bayyana cewa shi ne zai lashe zaben shugaban kasa a 2027.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

Rahotanni sun nuna cewa jagorar jam’iyyar NNPP ya yi wannan furuci ne a lokacin da ya kaddamar da sakatariyar jam’iyyar a Jihar Katsina kwanan nan.

ADVERTISEMENT

Tsohon gwamnan Jihar Kano, wanda Atiku da Obi suka yi zawarcinsa, ya ci gaba da cewa jam’iyyarsa ta NNPP a shirye take ta karbi ragamar shugabancin kasa, jihohi da sauran mukamai a fadin Nijeriya a zaben 2027.

Baya ga sanarwar tasa, Kwankwaso ya yi ikirarin cewa jam’iyyar PDP ta riga ta mutu, kuma ta fita daga kan layi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

“Ina so in tunatar da ku cewa jam’iyyar PDP ta riga ta mutu, saboda da muna cikin jam’iyyar, tun da suka fita daga kan layi, muka yanke shawarar barin jam’iyyar,” in ji shi.

Kafin kalamun na Kwankwaso, jam’iyyar PDP ta bayyana cewa manyan jiga-jigan ‘yan adawa na neman hadaka domin kalubalantar APC a zab0en 2027.

Mataimakin sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na asa, Ibrahim Abdullahi, ne ya bayyana haka a lokacin da yake tattaunawa a gidan talabijin na Channels.

Abdullahi ya tabbatar da cewa Atiku, Obi, da Kwankwaso suna tattaunawa kan yiwuwar yin kawance.

Ya koka da yadda jam’iyyar ta yi asarar kuri’u sama da miliyan daya, inda ya kara da cewa da Kwankwaso ko Obi sun ci gaba da zama a jam’iyyar, “da mun rufe gibi da kuma kauce wa matsalolin siyasa da tattalin arziki da ake ciki a yanzu.

“Tabbas. Ana ci gaba da tattaunawa. Kun ga Peter Obi yana tattaunawa da Atiku. Kun ga Peter Obi yana ganawa da el-Rufai,” inji Abdullahi, inda ya kara da cewa jam’iyyarsu na kokarin ganin Obi, Kwankwaso, da sauran shugabannin da suka bar PDP sun jam’iyyar kafin zaben 2027.

“Daya daga cikinsu zai yarda da sauran, sannan za mu sami alkibla. Damuwarmu a matsayin jam’iyya da kuma wadannan mutanen da na ambata shi ne za su ceto ‘yan Nijeriya daga irin wannan kunci da yunwa da fatara da rashin tsaro da ke damun kasar nan,” ya kara shaidawa.

Idan za a iya tuna kafin zaben 2023, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku, a wata hira da BBC, ya yi nuni da cewa akwai yiwuwar kawance da Obi da Kwankwaso, amma hakan bai faruwa ba.

Bugu da kari, an kuma samu rashin nasara a tattaunawar da aka yi kan kawance tsakanin Peter Obi na jam’iyyar LP da Rabiu Kwankwaso na NNPP, a daya bangaren.

Da yake magana a wata hira da ya yi da gidan talabijin na News Central, Obi ya ce ba ya neman shugabancin Nijeriya ta kowacce hanya.

Ya ce zai amince a yi aiki tare da wasu ne kawai idan ya ga mutanen da za su iya yin aikin da kyau.

A cewarsa, ba zai hada kai da kowa ba don manufar kama jihar ko kuma ya ci zabe.

Masana harkokin siyasa na nuna shakku kan kawancin Atiku da Kwankwaso da kuma Obi wajen kawar da jam’iyyar APC daga kan karagar mulkin Nijeriya. Wanda suke ganin kamar an samu matsala duba da irin kalamun da Kwankwaso ya furta da kuma irin martanin da PDP ta mayar masa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

December 19, 2025
‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

December 19, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Tambarin Dimokuradiyya

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

November 28, 2025
Next Post
Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.