• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masarautar Bwari Jiya Da Yau

by Idris Umar
3 years ago
in Rahotonni
0
bwari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Asabar din nan ne ake bai wa mai martaba Sarkin Bwari, Alhaji Awwal Musa Ijakoro sandan girma.

Bikin bayar da sandan girman wanda Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Mohammed Musa Bello zai shugabanta, zai gudana ne a Cibiyar Bunkasa Al’amuran Mata da ke Kuduru a yankin Bwari da ke Abuja.

  • Martanin Wike Ga Lamido: Ba Ka Da Sauran Wata Kima A Siyasa

Wanda ake sa ran farawa daga karfe 11 na safe, bikin zai samu halartar manyan baki da suka kunshi sarakuna, shugabannin siyasa da na al’umma da kuma sauran masu ruwa da tsaki.

Shin wanene mai martaba Alhaji Awwal Musa Ijakoro?
Mai girma Alhaji Awwal Musa Ijakoro, wani bawan Allah ne da za a ce al’ummar kasar Bwari da ke Abuja suka yi sa’ar samu a cikinsu kuma har ya zama sarki. Wannan duk yana daga cikin hikimar Allah.

Koda yake ya fito ne daga gidan sarauta tun asali, amma tun kafin ya zama sarki al’ummar kasar Bwari da dama suke girmama shi a matsayin shugaba wanda yeke da tausayin jama’a, kwarjini da ilmin sanin yadda ake zama lafiya da al’umma kamar yadda ya taso ya ga mahaifinsa na yi.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tarihi ya nuna cewa an haifi mai martaba Alhaji Awwal Musa Ijakoro ne a garin Bwari da ke Babban Birnin Tarayya Abuja, a ranar 9 ga watan Yunin shekarar 1977.

A ranar 24 ga watan Oktobar 2017 ne Ministan Abuja, Malam Mohammed Musa Bello ya nada Alhaji Awwal Musa Ijakoro a matsayin sabon Sarkin Bwari domin ya gaji mahaifinsa, Alhaji Muhammad Musa Ijakoro, da ya riga mu gidan gaskiya a ranar 29 ga Agustan 2017.

A hannun mahaifisa Alhaji Musa Muhammad Ijakoro ne masarautar ta zama mai daraja ta biyu a ranar 12 ga watan Yunin 1997.

Bincike ya nuna daukakar da masarautar tasu ta samu ta biyo bayan umurnin da marigayi shugaban kasa Janar Sani Abacha ya bai wa ministan Abuja na wancan lokacin ne Laftanar Janar Jeremiah Useni, da ya kara daukaka jdarajar masarautun da ke Birnin Tarayya Abuja.

A shekarun da mai martaba Alhaji Awwal Musa Ijakoro ya yi a kan karaga ya samu nasarar hada kan al’umarsa waje guda wanda hakan ya kawo zaman lafiya da daukaka a masarautar baki daya.

Dangane da batun ilmi kuma mai martaba Alhaji Awwal Musa Iajkoro ya yi karatun firamere ne a Suleja a shekarar 1984 zuwa 1989 a makarantar da ake kira Aliyu Wali. Sannan ya yi karatun sakandare a Makarantar GSS Kwali Abuja inda ya kammala a 1997.

Daga 2001 zuwa 2003 mai martaba ya yi karatun difuloma a kan harkokin gwamnati a Jami’ar Abuja wanda daga nan ne aka fara nada shi sarauta.

Ya kuma yi digiri a kan harkokin mulki (B.Sc Public Administration) a Jami’ar Nasarawa da ke Keffi. Kafin zaman sa Sarkin Bwari dai an nada shi Ciroman Bwari.

Ya yi aikin gwamnati musamman a makarantar Shari’a ta Nijeriya reshen Bwari daga 2000 zuwa 2010.

Kamar yadda Jagaban Shere Koro, Bala Ahmad Shere ya taba bayyana wa jaridar Daily Trust, “An daga darajar masarautar Bwari sama da shekara 25 da suka gabata tare da wasu hakimai na Birnin Tarayya Abuja.

Sun hada da Gundumomin Kwali da Kuje da sauran wasu masarautu na dagatai.
“Marigayi Dr. Musa Muhammad Ijakoro ya kasance wani basarake na daban a tsakanin wadanda suka mulki Bwari tun daga 1902 zuwa 1975. Bwari tana da dagatai guda 10 wadanda su ne suke zaben hakimi a Gundumar Bwari. Kuma a cikin wadannan dagatai akwai Koro, kuma akwai Gwari.”

Shi ma da yake jawabi, Ciroman Bwari, Abubakar Musa Ijakoro, ya bayyana cewa, biyo bayan ritayar dole da Gwamnan Soja na Jihar Arewa maso Yamma, Kwamishinan ‘yan sanda, Usman Faruk, ya yi wa Hakimin Bwari, Abubakar Barau Musa Angulu, a tsakanin shekarar 1954 zuwa 1975, an yi dokar soja da ta bayar da umurnin cewa a nada ‘yan asalin yanki a mukaman sarauta a gurabun da aka samar.

Ya ce yayin da aka bayar da damar fitowa domin neman kujerar Hakimin Bwari wadanda suka nema “sun hada da Malam Danladi Zuma – daga Bwari (Gbagyi), Samaila Mainasara – daga Ija-Gbagyi (Gbagyi), Salihu Sunbwada – daga Diko (Gbagyi), da Musa Muhammad – daga Ijakoro (Koro).

Ya yi nuni da cewa yayin da shugabannin kauyen Koro suka gabatar da dan takara daya tilo, sai su Gbagyi suka gabatar da ‘yan takara uku wadanda Ijakoro ya kayar da su.

“A halin da ake ciki, ya kamata duk duniya su sani cewa gundumar Bwari ba kawai ta kunshi Gbagyi da Koro da Hausawa da Fulani ne kadai ba. An kafa Zangon Hausawa na Bwari sama da shekara 89 kafin a tilasta wa Gbagyi su sauko daga tsauni.

“Hakazalika, muna so mu bayyana baro-baro a nan cewa Koro ya yi hijira zuwa Abuja da wuri tun kafin Gbagyi. Bisa ga takardun tarihi, duk inda ka ga Gbagyi, tabbas sun zo ne bayan Koro. Kuma sun girmama Koro. Shi ya sa Gbagyi kawai suke kiran Koro da ‘Apoyi’, ma’ana mai ceton rai.

Sarakunan Koro ne suka yi wa sarakunan Gbagyi rawani, wanda ke nufin sun kasance talakawan Koro a tsawon tarihin masarautar Abuja.

“Kafin zuwan ’yan mulkin mallaka da kuma bayan da Nijeriya ta samu ‘yancin kai a 1960; a koyaushe Dagacin Bwari ne yake nada Sarkin Dogon Kurmi.

Hakazalika, Hakimin kauyen Ushafa ya kasance Sarkin Ijakoro ne yake nada masa rawani,” ya bayyana.

Ciroman Bwari ya kuma ce dukkan abubuwan tarihi ko alamomin da ke Abuja mallakin Koro ne, ba wai Gwari da ke ikirarin mallakin Abuja ba.

Ya yi ikirarin cewa shahararren dutsen Aso Rock da Zuma Rock mallakin Koro ne. “Ko kuwa akwai wani Gbagyi da zai iya yin da’awar wadannan alamomin?” Ya tambaya.

Yayin hada wannan labarin ne kuma muka sami labarin rasuwar mahaifiyar mai martaba Alhaji Awwal Musa, da fatan Allah ya rahamshe ta, Allah ya bai wa mai martaba da sauran iyalanta hakurin jure rashin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dannau Ba Matsalar Aljanu Ba Ce, Aikin Kwakwalwa Ne -Dakta Maryam (Adon Gari)

Next Post

Yadda ‘Yan Kasuwar Kwari Ke Tafka Asara Saboda Ambaliyar Ruwa A Kano

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

3 weeks ago
Bwari
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

1 month ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 month ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 month ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Yadda ‘Yan Kasuwar Kwari Ke Tafka Asara Saboda Ambaliyar Ruwa A Kano

Yadda 'Yan Kasuwar Kwari Ke Tafka Asara Saboda Ambaliyar Ruwa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

Ƴan Arewa Za Su Yi Murna Idan Na Zama Shugaban Ƙasa — Peter Obi

July 7, 2025
AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

July 7, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.