• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Kasuwar Kwari Ke Tafka Asara Saboda Ambaliyar Ruwa A Kano

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Yadda ‘Yan Kasuwar Kwari Ke Tafka Asara Saboda Ambaliyar Ruwa A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan kasuwar Kantin Kwari a Jihar Kano sun koka kan asarar dukiyoyi da suka yi sakamakon ambaliyar ruwa.

Wannan na dauke me cikin wata tattaunawa da LEADERSHIP Hausa ta yi da ‘yan kasuwar, inda suka ce ‘yan kasuwa da dama suna kwashe kayayyakin da ke shagunansu.

  • Masarautar Bwari Jiya Da Yau
  • Dannau Ba Matsalar Aljanu Ba Ce, Aikin Kwakwalwa Ne -Dakta Maryam (Adon Gari)

Rahoton ya nuna cewa, ambaliyar ta afku ne bayan da aka yi ruwan sama kamar da bakin kwarya a daren ranar Laraba, yayin da aka toshe mafi yawan magudanan ruwa a kasuwar.

Wasu daga cikin ‘yan kasuwar da suka zanta da wakilinmu, sun danganta lamarin da rashin magudanan ruwa, da gina hanyoyin ruwa da kuma sabuwar gadar sama da aka gina a kusa da kasuwar.

Sun yi kira ga gwamnati da ta kawo musu dauki domin sun yi asarar kayayyakin na miliyoyin Naira.

Labarai Masu Nasaba

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

Kwamared Balarabe Tatari, shi ne shugaban kungiyar ‘yan kasuwa kanana da matsakaita na kantin kwarin, ya yi magana kan yadda suka yi hasashen faruwar irin wannan yanayi a lokacin da aka gina sabbin gine-gine a layin Ta’anbo da kuma layin Bayajidda.

Ya ci gaba da cewa, duk kokarin da kungiyar ta yi don ganin an yi wani abu game da lamarin ya ci tura. Ya ce rashin tsarin sufuri da hanyoyin ruwa a cikin kasuwar ya taimaka wajen ambaliya da sauran haduran muhalli.

Alhaji Balarabe ya bukaci gwamnati da masu ruwa da tsaki da su taimaka wa wadanda abin ya shafa tare da daukar matakin da ya dace domin dakile faruwar lamarin nan gaba.

A halin da ake ciki, shugaban hukumar da ke kula da Kantin Kwari, Alhaji Abba Muhammad Bello ya musanta cewa gine-ginen sun toshe hanyoyin ruwa.

Ya ce an rufe wasu magudanun ruwa ne na wani dan lokaci saboda aikin da ake yi a kasuwar.

Ya jaddada cewa hukumar za ta mika cikakken rahoto ga gwamnati domin daukar matakin da ya dace.

Idan za a iya tunawa, a watan Agustan 2021, ‘yan kasuwa a kasuwar Kantin Kwari sun gudanar da zanga-zangar lumana don nuna rashin gamsuwarsu da wani gini da ake ginawa a Layin Ta’anbo a cikin kasuwar.

Sun yi nuni da cewa layin Ta’anbo na daya daga cikin hanyoyin da ake amfani da su wajen safarar kayayyaki a cikin kasuwar sannan tasha ce da ke hada magudanun ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan KasuwaAmbaliyar RuwagwamnatikanoKantin KwariKasuwaMasu Ruwa Da Tsaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masarautar Bwari Jiya Da Yau

Next Post

Mai Martaba Sarkin Hadeja Zai Cika Shekara 20 Kan Karaga

Related

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

2 minutes ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

2 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

4 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da É—umi-É—uminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

6 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

9 hours ago
Next Post
hadeja

Mai Martaba Sarkin Hadeja Zai Cika Shekara 20 Kan Karaga

LABARAI MASU NASABA

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.