• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Kasuwar Kwari Ke Tafka Asara Saboda Ambaliyar Ruwa A Kano

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Yadda ‘Yan Kasuwar Kwari Ke Tafka Asara Saboda Ambaliyar Ruwa A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan kasuwar Kantin Kwari a Jihar Kano sun koka kan asarar dukiyoyi da suka yi sakamakon ambaliyar ruwa.

Wannan na dauke me cikin wata tattaunawa da LEADERSHIP Hausa ta yi da ‘yan kasuwar, inda suka ce ‘yan kasuwa da dama suna kwashe kayayyakin da ke shagunansu.

  • Masarautar Bwari Jiya Da Yau
  • Dannau Ba Matsalar Aljanu Ba Ce, Aikin Kwakwalwa Ne -Dakta Maryam (Adon Gari)

Rahoton ya nuna cewa, ambaliyar ta afku ne bayan da aka yi ruwan sama kamar da bakin kwarya a daren ranar Laraba, yayin da aka toshe mafi yawan magudanan ruwa a kasuwar.

Wasu daga cikin ‘yan kasuwar da suka zanta da wakilinmu, sun danganta lamarin da rashin magudanan ruwa, da gina hanyoyin ruwa da kuma sabuwar gadar sama da aka gina a kusa da kasuwar.

Sun yi kira ga gwamnati da ta kawo musu dauki domin sun yi asarar kayayyakin na miliyoyin Naira.

Labarai Masu Nasaba

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

Kwamared Balarabe Tatari, shi ne shugaban kungiyar ‘yan kasuwa kanana da matsakaita na kantin kwarin, ya yi magana kan yadda suka yi hasashen faruwar irin wannan yanayi a lokacin da aka gina sabbin gine-gine a layin Ta’anbo da kuma layin Bayajidda.

Ya ci gaba da cewa, duk kokarin da kungiyar ta yi don ganin an yi wani abu game da lamarin ya ci tura. Ya ce rashin tsarin sufuri da hanyoyin ruwa a cikin kasuwar ya taimaka wajen ambaliya da sauran haduran muhalli.

Alhaji Balarabe ya bukaci gwamnati da masu ruwa da tsaki da su taimaka wa wadanda abin ya shafa tare da daukar matakin da ya dace domin dakile faruwar lamarin nan gaba.

A halin da ake ciki, shugaban hukumar da ke kula da Kantin Kwari, Alhaji Abba Muhammad Bello ya musanta cewa gine-ginen sun toshe hanyoyin ruwa.

Ya ce an rufe wasu magudanun ruwa ne na wani dan lokaci saboda aikin da ake yi a kasuwar.

Ya jaddada cewa hukumar za ta mika cikakken rahoto ga gwamnati domin daukar matakin da ya dace.

Idan za a iya tunawa, a watan Agustan 2021, ‘yan kasuwa a kasuwar Kantin Kwari sun gudanar da zanga-zangar lumana don nuna rashin gamsuwarsu da wani gini da ake ginawa a Layin Ta’anbo a cikin kasuwar.

Sun yi nuni da cewa layin Ta’anbo na daya daga cikin hanyoyin da ake amfani da su wajen safarar kayayyaki a cikin kasuwar sannan tasha ce da ke hada magudanun ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan KasuwaAmbaliyar RuwagwamnatikanoKantin KwariKasuwaMasu Ruwa Da Tsaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masarautar Bwari Jiya Da Yau

Next Post

Mai Martaba Sarkin Hadeja Zai Cika Shekara 20 Kan Karaga

Related

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
Kasashen Ketare

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

1 hour ago
Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga
Labarai

Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

2 hours ago
Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu
Manyan Labarai

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

4 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

7 hours ago
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

18 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

20 hours ago
Next Post
hadeja

Mai Martaba Sarkin Hadeja Zai Cika Shekara 20 Kan Karaga

LABARAI MASU NASABA

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

July 13, 2025
Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

July 13, 2025
Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

July 13, 2025
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

July 13, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

July 13, 2025
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

July 13, 2025
Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.