ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Hukuncin Yin Jam’i Na Biyu A Masallacin Da Ke Da Limami Ratibi 

by Ibrahim Bala
2 weeks ago
Hukuncin

Assalamu alaikum. Malam, mene ne hukuncin sallar mutanen da suka tarar an idar da sallah a masallacin da ke da tabbataccen limami, suka yi tasu sallar a jam’i?

Wa’alaikum assalam. Malamai sun cimma daidaito a kan halaccin yin jam’i biyu a masallacin da ba shi limami Ratibi, kamar masallacin tasha da na kan hanya, sai dai sun ƙara wa juna sani game da masallacin da yake da tabbataccen limami zuwa zantuka guda biyu:

  • Sarki Sanusi II Ya Yi Hawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda Na Haramta Hawan Sallah A Kano
  • Fityanul Islam Ta Nesanta Kanta Daga Zanga-zangar Da Ake Shirin Yi
  1. Makaruhi ne yin hakan, saboda Annabi SAW ya taɓa zuwa masallacinsa mai alfarma, sai ya samu an yi sallah, sai ya juya, ya yi sallah a gida, Haisami ya ambaci wannan hadisin a cikin Majma’uzzawa’id, kuma ya ce; maruwaitan hadisin amintattu ne.
  2. Mustahabbi ne yin jam’i na biyu a masallacin da yake da limami Ratibi, sun kafa hujja da hadisin da wani mutum ya zo masallacin Harami, bayan an gama sallah, sai Manzon Àllah ya ce; “Wane ne zai yi sadaka ga wannan mutumin, ya yi sallah tare da shi”?, sai wani sahabi ya tashi ya taimaka masa, suka yi sabon jam’i da izinin Manzon Tsira SAW, kamar yadda Abu Dawud da Tirmizi suka rawaito.

Magana ta biyu ta fi inganci, saboda nassin da suka kafa hujja da shi kaifi ɗaya ne, ga kuma tarin hadisan da suke magana a kan falalar sallar jam’i.

ADVERTISEMENT

A ilimin USULU, nassin da yake kaifi ɗaya; ana gabatar da shi a kan nassin da yake ɗaukar sama da ma’ana ɗaya.

Komawar Annabi SAW gida, yana ɗaukar fuskoki da yawa, zai yiwu Manzon tsira ya koma gida ne, saboda duba maslaha, da ya yi jam’i na biyu, da wasu sun sake sallah, hakan kuma yana iya buɗe ƙofar zace-zace a kan limamin farko.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Shugaban Ƙasa Ta Isa Bauchi Don Jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

Allah ne mafi sani.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Shugaban Ƙasa Ta Isa Bauchi Don Jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi
Addini

Tawagar Shugaban Ƙasa Ta Isa Bauchi Don Jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi

November 28, 2025
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)
Addini

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

July 4, 2025
Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli
Addini

Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli

June 22, 2025
Next Post
Sojojin Sin Da Rasha Sun Yi Atisayen Dakile Harin Makamai Masu Linzami

Sojojin Sin Da Rasha Sun Yi Atisayen Dakile Harin Makamai Masu Linzami

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.