Ma’aikatar tsaron kasar Sin ta ce sojojin kasar da takwarorinsu na kasar Rasha sun yi wani atisayen soja na dakile harin makamai masu linzami, irinsa na 3, a farkon watan Disamban da muke ciki, a kasar Rasha.
Ban da haka, sanarwar da ma’aikatar tsaron ta fitar jiya Asabar ta shafin intanet ta kara da cewa, wannan atisayen soja ba ya nufin matsawa wani bangare lamba, kuma babu ruwansa da yanayin siyasa da ake ciki a wasu yankuna, da ma duk duniya baki daya. (Bello Wang)
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
ADVERTISEMENT














