• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

A woman votes at a polling station in Kano, Nigeria, March 28, 2015. Many Nigerians fear a clash along religious, ethnic, and sectional lines regardless of the result of the presidential race between incumbent Goodluck Jonathan, a Christian from the south, and Muhammadu Buhari, a former military ruler and Muslim northerner. (Samuel Aranda/The New York Times)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ko da yaushe zabe a Nijeriya ya kan kasance ne bisa la’akari da kuri’un da ake jefawa a yankuna.

Wannan lamari ne da ke turnike zaben kasar nan tun a shekarar 1959 lokacin da yankin arewa ya fi samun kujeru masu yawa da aka amince na yin sulhu wajen hawa karagar mulki.

  • Kashi 31 Na ‘Yan Nijeriya Ba Su Iya Karatu Da Rubutu Ba ― Gwamnatin Tarayya
  • Kwastam Ta Damke Mazakutar Jaki 7000 Da Miyagun Kwayoyi A Legas

Tun bayan da kawo mulkin dimokuradiyya, yankin arewa yana taka muhimmin rawa a cikin harkokin dimokuradiyyar kasar nan.

Mafi yawancin shugabannin da suka lashe zabe dole ne sai sun samu nasara a yankin arewa maso yammacin Nijeriya, duk da ba shi ne samun nasara na karshe a zabe ba.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dade yana samun nasara a yankin arewa maso yamma, tun a shekarar 2003 mafi yawancin abokan karawarsa suna faduwa zabe a wannan yankin.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

Yankin arewa maso yamma ta hada wasu jihohin da suke da harafin K har guda hudu, Kano, Kaduna, Katsina da Kebbi, wanda suke iya samar wa dan takara sama da kuri’u miliyan uku, wannan ya danganta ne da yanayin dan takarar.

Mafi yawancin ‘yan takara suna lashe zabe ne a tsakanin kuri’u miliyan 15 zuwa 17, sai dai Jonathan da ya samu kuri’u miliyan 20, wanda ba a taba samu ba tun bayan shekaru 10 da suka gabata.

Yankin arewa maso yamma ya kasance yankin da ake bai wa ‘yan takara dauki, sai dai kabalanci da addini suna taka muhimmiyar rawa a yankin.

Ba za a taba musanta cewa ‘yan Nijeriya suna amfani da kabila da addini wajen zaben dan takara ba.

Sai dai abin da yafi dacewa shi ne, samun kasa daya ba tare da la’akari da yanki ko addini ba.

Abun tambaya a nan shi ne, ina kuri’an yankin arewa maso yamma za su kasance? Wasu na ganin cewa Tinunbu yana da tabbacin lashe wannan yankin, amma tambayan ita ce, ta ina zai iya samun nasarar? Wannan lokaci ne kadai zai iya tabbatar da haka.

Wasu na ganin cewa an samu sauyin jefa kuri’a a yankin arewa maso yamma sakamakon irin kiraye-kirayen da malaman addini ke yi.

Haka kuma wasu ‘yan siyasa a yankin arewa sun dage a kan sai mulki ya dawo arewa ta hannun Atiku, inda suka tabbatar da cewa kuri’un yankin arewa maso yamma za su kasance na Atiku ne.

Wasu kuma na ganin Peter Obi da Kwankwaso na iya taka rawa a wannan yankin. Bayan addni da kala da suke da tasiri a yankin arewa maso yamma, kudade ma za su taka muhimmiyar rawa a yankin.

Wasu na ganin cewa wannan ita ce siyasa mafi tsada da za a gudanar a kasar nan.

A yanzu da ya rage saura kasa da kwani 170 a gudanar da zabe, abu guda daya shi ne, duk wanda ya lashe yankin arewa maso yamma shi zai ci nasara a zabe? Lokaci ne kadai zai iya tabbatar da haka.

A yawan masu rajista da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta fitar, yankin arewa maso yamma shi ke kan gaba, inda yake da yawan masu jefa kuri’a guda 22,672,373.

Wannan bayani yana cikin shafin hukumar INEC, inda ta nuna cewa ta samu karin masu rajistar zabe guda 12,298,932 a zaben 2023.

Gaba daya jimillar jihohin arewa masu yamma sun hada da Jigawa, Kaduna, Katsina, Kano, Kebbi, Sakkwato da kuma Zamfara, da suke da yawan masu jefa kuri’a guda 22,672,373 a zaben 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaArewa Maso YammaSiyasaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masoyan Takai Da Gawuna Za Su Mara Wa Tinubu A 2023

Next Post

Shugaba Xi Ya Taya João Lourenço Murnar Lashe Zaben Shugaban Angola

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

2 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

2 days ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

2 days ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
Next Post
Shugaba Xi Ya Taya João Lourenço Murnar Lashe Zaben Shugaban Angola

Shugaba Xi Ya Taya João Lourenço Murnar Lashe Zaben Shugaban Angola

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final

Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final

July 6, 2025
Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund

Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund

July 6, 2025
Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

July 6, 2025
Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

July 6, 2025
Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

July 6, 2025
Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.