• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

A woman votes at a polling station in Kano, Nigeria, March 28, 2015. Many Nigerians fear a clash along religious, ethnic, and sectional lines regardless of the result of the presidential race between incumbent Goodluck Jonathan, a Christian from the south, and Muhammadu Buhari, a former military ruler and Muslim northerner. (Samuel Aranda/The New York Times)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ko da yaushe zabe a Nijeriya ya kan kasance ne bisa la’akari da kuri’un da ake jefawa a yankuna.

Wannan lamari ne da ke turnike zaben kasar nan tun a shekarar 1959 lokacin da yankin arewa ya fi samun kujeru masu yawa da aka amince na yin sulhu wajen hawa karagar mulki.

  • Kashi 31 Na ‘Yan Nijeriya Ba Su Iya Karatu Da Rubutu Ba ― Gwamnatin Tarayya
  • Kwastam Ta Damke Mazakutar Jaki 7000 Da Miyagun Kwayoyi A Legas

Tun bayan da kawo mulkin dimokuradiyya, yankin arewa yana taka muhimmin rawa a cikin harkokin dimokuradiyyar kasar nan.

Mafi yawancin shugabannin da suka lashe zabe dole ne sai sun samu nasara a yankin arewa maso yammacin Nijeriya, duk da ba shi ne samun nasara na karshe a zabe ba.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dade yana samun nasara a yankin arewa maso yamma, tun a shekarar 2003 mafi yawancin abokan karawarsa suna faduwa zabe a wannan yankin.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Yankin arewa maso yamma ta hada wasu jihohin da suke da harafin K har guda hudu, Kano, Kaduna, Katsina da Kebbi, wanda suke iya samar wa dan takara sama da kuri’u miliyan uku, wannan ya danganta ne da yanayin dan takarar.

Mafi yawancin ‘yan takara suna lashe zabe ne a tsakanin kuri’u miliyan 15 zuwa 17, sai dai Jonathan da ya samu kuri’u miliyan 20, wanda ba a taba samu ba tun bayan shekaru 10 da suka gabata.

Yankin arewa maso yamma ya kasance yankin da ake bai wa ‘yan takara dauki, sai dai kabalanci da addini suna taka muhimmiyar rawa a yankin.

Ba za a taba musanta cewa ‘yan Nijeriya suna amfani da kabila da addini wajen zaben dan takara ba.

Sai dai abin da yafi dacewa shi ne, samun kasa daya ba tare da la’akari da yanki ko addini ba.

Abun tambaya a nan shi ne, ina kuri’an yankin arewa maso yamma za su kasance? Wasu na ganin cewa Tinunbu yana da tabbacin lashe wannan yankin, amma tambayan ita ce, ta ina zai iya samun nasarar? Wannan lokaci ne kadai zai iya tabbatar da haka.

Wasu na ganin cewa an samu sauyin jefa kuri’a a yankin arewa maso yamma sakamakon irin kiraye-kirayen da malaman addini ke yi.

Haka kuma wasu ‘yan siyasa a yankin arewa sun dage a kan sai mulki ya dawo arewa ta hannun Atiku, inda suka tabbatar da cewa kuri’un yankin arewa maso yamma za su kasance na Atiku ne.

Wasu kuma na ganin Peter Obi da Kwankwaso na iya taka rawa a wannan yankin. Bayan addni da kala da suke da tasiri a yankin arewa maso yamma, kudade ma za su taka muhimmiyar rawa a yankin.

Wasu na ganin cewa wannan ita ce siyasa mafi tsada da za a gudanar a kasar nan.

A yanzu da ya rage saura kasa da kwani 170 a gudanar da zabe, abu guda daya shi ne, duk wanda ya lashe yankin arewa maso yamma shi zai ci nasara a zabe? Lokaci ne kadai zai iya tabbatar da haka.

A yawan masu rajista da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta fitar, yankin arewa maso yamma shi ke kan gaba, inda yake da yawan masu jefa kuri’a guda 22,672,373.

Wannan bayani yana cikin shafin hukumar INEC, inda ta nuna cewa ta samu karin masu rajistar zabe guda 12,298,932 a zaben 2023.

Gaba daya jimillar jihohin arewa masu yamma sun hada da Jigawa, Kaduna, Katsina, Kano, Kebbi, Sakkwato da kuma Zamfara, da suke da yawan masu jefa kuri’a guda 22,672,373 a zaben 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaArewa Maso YammaSiyasaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masoyan Takai Da Gawuna Za Su Mara Wa Tinubu A 2023

Next Post

Shugaba Xi Ya Taya João Lourenço Murnar Lashe Zaben Shugaban Angola

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

3 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

4 weeks ago
Next Post
Shugaba Xi Ya Taya João Lourenço Murnar Lashe Zaben Shugaban Angola

Shugaba Xi Ya Taya João Lourenço Murnar Lashe Zaben Shugaban Angola

LABARAI MASU NASABA

Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

August 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

August 11, 2025
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

August 11, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.