• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan APC Ne Ke Ruruta Wutar Sai Ayu Ya Sauka –Dino Melaye

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
APC

Mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, Sanata Dino Melaye ya bayyana cewa ‘yan APC ne ke kara ruruwa wutar rikicin sai an cire shugaban jam’iyyar PDP, Dakta Iyorchia Ayu kafin zaben 2023.

Melaye ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa a dakin watsa shirye-shirye na LEADERSHIP da ke Abuja.

  • Kotu Ta Soke Takarar Dare A Matsayin Wanda Zai Yi Wa PDP Takarar Gwamna A Zamfara

Ya kara da cewa ‘yan APC suna kokarin tarwatsa tsarin mulkin jam’iyyar PDP, shi ya sa suka dage a kan sai an saukar da Ayu daga mukaminsa.

Melaye ya koka kan yadda jam’iyyar PDP ta samu kanta a rikicin cikin gida, amma duk da haka yana da tabbacin cewa Atiku ne zai lashe zaben shugaban kasa na 2023.

Shi dai Ayu ya ki amincewa da bukatar Gwamna Jihar Ribas, Nyesom Wike na ya sauka daga shugabancin jam’iyyar a matsayin sharadi da zai mara wa Atiku baya a zaben 2023.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Ya ce, “Wadanda suka dage sai an cire Ayu daga shugabancin PDP, ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke kokarin tarwatsa tsarin mulkin PDP domin APC ta amfana.

“Idan muka duba tsarin mulkin jam’iyyarmu, in har aka cire shugaban jam’iyyar, to dole a maye gurbinsa da wani da suke yankin daya. A yau idan har Ayu ya sauka, mataimakinsa daga yankin arewa ne zai gaje shi.

“Kuma suna adawa ne kan dan arewa bai kamata ya zama shugaban jam’iyyar ba, sannan dan takarar shugaban kasa ya kasance dan arewa, amma hakan ya taba faruwa a baya lokacin da dan arewa yake shugabancin jam’iyyar aka zabi Goodluck Jonathan, sa’ilin da aka rantsar da Jonathan sai aka cire shi nan take.

“Mu ba mu ce Ayu ya ci gaba da shugabancin jam’iyyar lokacin da aka zabi Atiku a matsayin shugaban kasa ba. Lokacin da Atiku ya samu nasara a zabe, to dole Ayu ya sauka daga shugabancin jam’iyyar.

“Lokacin da muka zabi Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar, kowa ya san daga yankin Arewa ya fito, an dai zabe shi ne bisa cancanta da zai iya magance matsalolin jam’iyyar.
“Bisa haka, nake cewa babu wata matsala. Jam’iyyar PDP ta kasance tana da kyakkyawan tsari da muke tabbatar da cewa kowa ana ba shi hakkinsa,” in ji shi.
Mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben Atiku ya dage da cewa dan karamin rashin jituwa ne aka samu tsakanin bangarori guda biyu na jam’iyyar wanda ake samu a cikin harkokin dimokuradiyya.
A cewarsa, matsala da aka samu da Wike nan da ‘yan kwanaki komai zai daidaita, domin ita PDP jam’iyya ce mai hada kan ‘ya’yanta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Yadda Jami’an Ma’aikatar Kudi Suka Sace Kudin Wani Marigayi Ta POS A Bauchi

Yadda Jami’an Ma’aikatar Kudi Suka Sace Kudin Wani Marigayi Ta POS A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.