• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan APC Ne Ke Ruruta Wutar Sai Ayu Ya Sauka –Dino Melaye

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan APC Ne Ke Ruruta Wutar Sai Ayu Ya Sauka –Dino Melaye
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, Sanata Dino Melaye ya bayyana cewa ‘yan APC ne ke kara ruruwa wutar rikicin sai an cire shugaban jam’iyyar PDP, Dakta Iyorchia Ayu kafin zaben 2023.

Melaye ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa a dakin watsa shirye-shirye na LEADERSHIP da ke Abuja.

  • Kotu Ta Soke Takarar Dare A Matsayin Wanda Zai Yi Wa PDP Takarar Gwamna A Zamfara

Ya kara da cewa ‘yan APC suna kokarin tarwatsa tsarin mulkin jam’iyyar PDP, shi ya sa suka dage a kan sai an saukar da Ayu daga mukaminsa.

Melaye ya koka kan yadda jam’iyyar PDP ta samu kanta a rikicin cikin gida, amma duk da haka yana da tabbacin cewa Atiku ne zai lashe zaben shugaban kasa na 2023.

Shi dai Ayu ya ki amincewa da bukatar Gwamna Jihar Ribas, Nyesom Wike na ya sauka daga shugabancin jam’iyyar a matsayin sharadi da zai mara wa Atiku baya a zaben 2023.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Ya ce, “Wadanda suka dage sai an cire Ayu daga shugabancin PDP, ‘ya’yan jam’iyyar APC ne da ke kokarin tarwatsa tsarin mulkin PDP domin APC ta amfana.

“Idan muka duba tsarin mulkin jam’iyyarmu, in har aka cire shugaban jam’iyyar, to dole a maye gurbinsa da wani da suke yankin daya. A yau idan har Ayu ya sauka, mataimakinsa daga yankin arewa ne zai gaje shi.

“Kuma suna adawa ne kan dan arewa bai kamata ya zama shugaban jam’iyyar ba, sannan dan takarar shugaban kasa ya kasance dan arewa, amma hakan ya taba faruwa a baya lokacin da dan arewa yake shugabancin jam’iyyar aka zabi Goodluck Jonathan, sa’ilin da aka rantsar da Jonathan sai aka cire shi nan take.

“Mu ba mu ce Ayu ya ci gaba da shugabancin jam’iyyar lokacin da aka zabi Atiku a matsayin shugaban kasa ba. Lokacin da Atiku ya samu nasara a zabe, to dole Ayu ya sauka daga shugabancin jam’iyyar.

“Lokacin da muka zabi Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar, kowa ya san daga yankin Arewa ya fito, an dai zabe shi ne bisa cancanta da zai iya magance matsalolin jam’iyyar.
“Bisa haka, nake cewa babu wata matsala. Jam’iyyar PDP ta kasance tana da kyakkyawan tsari da muke tabbatar da cewa kowa ana ba shi hakkinsa,” in ji shi.
Mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben Atiku ya dage da cewa dan karamin rashin jituwa ne aka samu tsakanin bangarori guda biyu na jam’iyyar wanda ake samu a cikin harkokin dimokuradiyya.
A cewarsa, matsala da aka samu da Wike nan da ‘yan kwanaki komai zai daidaita, domin ita PDP jam’iyya ce mai hada kan ‘ya’yanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Za Ta Kafa Hukumar Kula Da Magungunan Gargajiya

Next Post

Yadda Jami’an Ma’aikatar Kudi Suka Sace Kudin Wani Marigayi Ta POS A Bauchi

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Yadda Jami’an Ma’aikatar Kudi Suka Sace Kudin Wani Marigayi Ta POS A Bauchi

Yadda Jami’an Ma’aikatar Kudi Suka Sace Kudin Wani Marigayi Ta POS A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

July 2, 2025
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

July 2, 2025
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

July 2, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

July 2, 2025
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.