• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
3 years ago
in Rahotonni
0
Bukatar Kawo Karshen Rushewar Gine-gine A Nijeriya (Ra’ayinmu)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani abu mai tayar da hankali a bangaren gine-gine a Nijeriya a wannan lokacin yanzu wanda a lokutan-baya sai dai a ji labari dai-dai amma yanzu al’amarin ya zama ruwan dare, shi ne annobar rushewar gine-gine, wanda hakan ke nuna irin matsalar da bangaren gine-gine na Nijeriya ya shiga.

Rahotanni daga sassan kasar nan suna nuna yadda ake samun rugujewar gine-gine abin da ke kai ga asarar rayukar al’umma da dukiyoyin mutane da dama, mutane sun zura ido ga gwamnagti don ta samu musu mafita na yadda masu ruwa da tsaki da harkar gine-gine za su tabbatar da bin doka da oda a harkokinsu.

  • DA DUMI-DUMI: Wani Gini Mai Hawa 7 Ya Rushe A Legas

Zuwa yanzu rushewar gine-ginen da aka samu a baya ba mu ji labarin gwamnati ta dauki matakin hukunta masu hannu a kan faruwar lamarin ba, da kuma jami’an gwamnati wadanda su ke bayar da izinin yin gine-ginen da kaya marasa inganci.

Idan za a iya tunawa, a watan Satumba, mutum biyu sun mutu yayin da ma’aikata 4 suka makale a karkashin baraguzai a yayin da wani bene mai hawa 2 ya rushe a unguwar Oba Abiodun Oniru a yankin rukunin gidaje na Oniru, a Lekki ta Jihar Legas.

Yakamata ya yi a lura da cewa, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, LASEMA, ta bayyana cewa, gidaje 30 suka rushe a sassa daban-daban na Jihar Legas a tsakanin watan Janairu zuwa Yuli na 2022.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Kididdiga ta baya bayan nan, kamar yadda Babban Sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas, Dakta Femi Oke-Osanyitolu ya nuna, ya ce, daga cikin kiran gaggawa 973 da aka yi musu mafi yawa na rugujewar gine-gine ne, an kuma fi samun wadannan kiraye-kiraye na gaggawan ne daga karamar hukumar Alimosho inda aka samu gidaje 24 da suka ruguje gaba daya da gidaje 6 da wani bangare nasu ya ruguje da kuma wani gida da yake dab da rushewa.

Hakanan kuma, rahotanni daga kafafen watsa labarai na nuna cewa, akalla mutum 84 suka rasa rayukansu a cikin gidaje 18 da suka rushe a Jihar Legas a cikin shekara 2 da suka wuce.

Kusan mako 4 kenan da rushewar wani bene mai hawa 4 a yankin Bodija da ke Ibadan a Jihar Oyo sai kuma gashi wani bene mai hawa 2 ya sake rushewa a yankin da ake magana a daren ranar Lahadin da ta wuce.

A watan da ya gabata, wani bene mai hawa 4 ya rushe a Uyo, babbar birnin Jihar Akwa Ibom inda mutane da dama suka makale a cikin baraguzan ginin.

A watan Agusta kuma, wani mutum ya mutu bayan da wani bene mai tsawo ya rushe a garin Kano inda wasu da dama suka makale. An tabbatar da mutuwar mutum biyu a watan Agusta a yayin da wani bene mai hawa 3 ya rushe a garin Kubwa da ke yankin babban birnin tarayya Abuja.

A ra’ayin wannan jaridar, muna iya cewa, a halin yanzu muna fuskantar annobar rushewar gine-gine ne a kasar nan. Abin takaicin kuma shi ne, daga shekarar 1974 zuwa watan Yuli na shekarar 2021, kididdiga ta nuna cewa, gidaje 461 suka rushe a Nijeriya inda fiye da mutum 1,090 suka mutu wasu kuma suka rasa rayukansu.

A ‘yan shekarun nan an samu rushewar gini 295 a Jihar Legas, Abuja 16, Oyo, 16, Anambra 15, Kano 9, Ondo 10, Abia 9, Kwara 8, Ribers 8, Delta 8, Enugu 7, Ogun 7, Plateau 6, Kaduna 6, Edo 6, Imo 5, Osun 5, Benue 3, Adamawa 3, a Jihar Ebonyi kuma guda 3. An samu rushewar gini 2 a Neja, Kebbi 2, Ekiti 2, Cross Riber 2, Sokoto 1, Bauchi 1, Akwa-Ibom, Kogi 1, Jihar Katsina kuma gini 1.

Masana sun dora alhakin yawan rushewar gine-ginen kan yadda ake amfani da kayan aiki marasa inganci da rashin bin ainihin taswirar da aka samar don ginin da kuma rashin yin binciken da ya kamata a a kan yanayin kasar da za a yi ginin a kai, bugu da kari kuma amfani da baragurbin ma’aikata wadanda ba su da kwarewar da ta kamata na haifar da irin wannan matsalar ta rushewar gine-gine.

Muna kira da gwamnati da a tabbatar da an gano tare da hukunta dukkan kwararrun da ke da hannu a gidajen da suka rushe da wadanda suka zuba jari a harkar ginin da ya rushe, wannan zai zama darasi ga masu daukar aikin da ya rataya a kan da muhimmanci.

Ya kuma kamata gwamnati ta tabbatar da bin dokoki da ka’idojin da ke tattare da gine-gine a Nijeriya tare da hukunta duk wani jami’in da aka samu yana sakosako da ayyukansa wanda hakan ya kai ga rushewar gini a fadin tarayyar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

DA DUMI-DUMI: An Sanya Wa ‘Yan Nijeriya Dokar Hana Samun Izinin Shiga Dubai

Next Post

Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

3 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

3 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

4 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

4 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

1 month ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

1 month ago
Next Post
Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

Wakilan Amurka Da Rasha Sun Tattauna Kan Batun Yakin Ukraine

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

August 13, 2025
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin ÆŠan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 FyaÉ—e A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 FyaÉ—e A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.