• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan ma’aikatar noma da raya karkara Dakta Mohammed Mahmood Abubakar ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya na aiki da hukumar yaki da fasakwari domin a dakile shigo da abinci daga kasashen ketare zuwa cikin kasar nan.

Dakta Mohammed ya sanar da hakan ne a jawabinsa yayin ziyarar aiki da ya kai a shalkwatar cibiyar binciken ‘ya’yan itatuwa (NIHORT) da ke garin Ibadan cikin jihar Oyo.

  • Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe
  • Abokai Na Zahiri Suna Zurfafa Huldar Zumunci A Sabon Zamani

A cewar Dakta Mohammed, a cikin shirye-shiyen da gwamnatin tarayya ke kan yi domin ta tabbatar Nijeriya ba ta fuskanci karancin abinci ba, ma’aikarar ta fara shirin fara gudanar da aikin noman rani wanda za a fara a cikin wata mai zuwa, inda ya yi nuni da cewa, fannin aikin noma shi ne na daya da ke kara habaka fannin tattalin arzikiin kasar nan.

A cewar Dakta Mohammed,“Zamu tabbatar daukacin hukumomin gwamnati na yin aiki kafada da kafada da hukumar kwastam da muke yin aiki da su, kamar hukumar kwastam domin a tabbatar ba a shigo da abinci ta barauniyar hanya zuwa cikin kasar nan ba domin ba ma son mu samu karancin abinci a kasar nan, inda ya kara da cewa, a yanzu ba ma karancin abinci a kasar nan, muna da wadataccen abinci.

Ministan ya sanar da cewa, shugaban kasa Muhammadu Buhari na bai wa ma’aikatar taimakon da ya dace, domin yana taimaka wa fannin aikin noma ta bayar da gagarumar gudunmowa wajen kara bunkasa tattalin arzikin Nijeriya, inda kuma ya bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa, gwamnatin tarayya za ta ci gaba kara kara bayar da gudunmawa domin cibiyar ta kara fadada gudanar da binciken don a kara bunkasa fannin oma a kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

“A yanzu ba ma karancin abinci a kasar nan, muna da wadataccen abinci a kasar nan”.

A taron, Dakta Mohammed ya kuma mika ingantacen irin Kubewa da cibiyar ta NIHORT ta samar gaingantaccen ga sashen bunkasa aikin noma (ADPs) da kuma ga wakilin kungiyoyi masu zaman kansu dake suka fito daga jihohin Oyo, Osun da Ogun.

A na sa jawabin tunda farko, shugaban cibiyar NIHORT Dakta Muhammed Attanda ya godewa ministan, musamman bisa taimakon da cibiyar ke ci gaba da samu daga ma’aikatar noma, inda ya ce, cibiyar ta gudanar da hakan ne domin jin ta bakin manoman a kan irin ingancin irin noma da cibiyar ke samar wa manoman.

Dakta Attanda ya kara da cewa, wannan aiki ne da cibiyar ta saba gudanar wa duk shekara, muna kuma kiran aikin a matsayin yin nazari dangane da irin binciken da cibiyar ta gudanar a fannin aikin noma, musamman domin mu ji ra’ayoyin manoman a kan irin noman ga cibiyar ta samar.

“Cibiyar ta gudanar da hakan ne domin jin ta bakin manoman a kan ingancin irin noma da cibiyar ke samar wa manoman”.

A na sa jawabin, shugaba kungiyar bunkasa noman mknoma ta kasa reashen jihar Oyo (ADFA) Alhaji Salihu Imam ya yaba wa cibiyar ta NIHORT kan taimaka wa manoma, inda ya yi ikirarin cewa, cibiyar ce kadai, da ta samar wa da manoman da kadada daga 30 zuwa 40 don yin noma ba tare da biyan wani kudin hayar gona ba.

“Cibiyar ce kadai, da ta samar wa da manoman da kadada daga 30 zuwa 40 don yin noma ba tare da biyan wani kudin hayar gona ba”.

Ita ma jami’ar shirin na JDPC ta reshen garin Ibadan, uwargida Adebola Ojewale, wacce kuma tana daya daga cikin wadanda suka amfana ta nuna jin dadinta akan amfanar da suke yi da cibiyar.

Adebola Ojewale ta sanar da cewa,” Na ji dadi matuka domin ko a kwanan baya, manoma na sayo irin noman ne a kasuwanni wadanda akasarin irin, ba shi da ingancin da ake bukata, amma ina da yakinin ganin cewa wamnan irin ya fito ne daga cibiyar, ba ni da wata tantama a kansa”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IyakaMinistaNomaShinkafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Fitar Da Sabon Bayani Kan Murar Tsintsaye

Next Post

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

Related

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

1 day ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

1 day ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

1 week ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

1 week ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

1 week ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.