• Leadership Hausa
Monday, February 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Noma Da Kiwo

Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

by Abubakar Abba
2 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

Ministan ma’aikatar noma da raya karkara Dakta Mohammed Mahmood Abubakar ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya na aiki da hukumar yaki da fasakwari domin a dakile shigo da abinci daga kasashen ketare zuwa cikin kasar nan.

Dakta Mohammed ya sanar da hakan ne a jawabinsa yayin ziyarar aiki da ya kai a shalkwatar cibiyar binciken ‘ya’yan itatuwa (NIHORT) da ke garin Ibadan cikin jihar Oyo.

  • Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe
  • Abokai Na Zahiri Suna Zurfafa Huldar Zumunci A Sabon Zamani

A cewar Dakta Mohammed, a cikin shirye-shiyen da gwamnatin tarayya ke kan yi domin ta tabbatar Nijeriya ba ta fuskanci karancin abinci ba, ma’aikarar ta fara shirin fara gudanar da aikin noman rani wanda za a fara a cikin wata mai zuwa, inda ya yi nuni da cewa, fannin aikin noma shi ne na daya da ke kara habaka fannin tattalin arzikiin kasar nan.

A cewar Dakta Mohammed,“Zamu tabbatar daukacin hukumomin gwamnati na yin aiki kafada da kafada da hukumar kwastam da muke yin aiki da su, kamar hukumar kwastam domin a tabbatar ba a shigo da abinci ta barauniyar hanya zuwa cikin kasar nan ba domin ba ma son mu samu karancin abinci a kasar nan, inda ya kara da cewa, a yanzu ba ma karancin abinci a kasar nan, muna da wadataccen abinci.

Ministan ya sanar da cewa, shugaban kasa Muhammadu Buhari na bai wa ma’aikatar taimakon da ya dace, domin yana taimaka wa fannin aikin noma ta bayar da gagarumar gudunmowa wajen kara bunkasa tattalin arzikin Nijeriya, inda kuma ya bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa, gwamnatin tarayya za ta ci gaba kara kara bayar da gudunmawa domin cibiyar ta kara fadada gudanar da binciken don a kara bunkasa fannin oma a kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

Nijeriya Na Samun Fiye Da Dala Miliyan 250 Daga Kashun Da Ake Fitarwa Waje -Minista

“A yanzu ba ma karancin abinci a kasar nan, muna da wadataccen abinci a kasar nan”.

A taron, Dakta Mohammed ya kuma mika ingantacen irin Kubewa da cibiyar ta NIHORT ta samar gaingantaccen ga sashen bunkasa aikin noma (ADPs) da kuma ga wakilin kungiyoyi masu zaman kansu dake suka fito daga jihohin Oyo, Osun da Ogun.

A na sa jawabin tunda farko, shugaban cibiyar NIHORT Dakta Muhammed Attanda ya godewa ministan, musamman bisa taimakon da cibiyar ke ci gaba da samu daga ma’aikatar noma, inda ya ce, cibiyar ta gudanar da hakan ne domin jin ta bakin manoman a kan irin ingancin irin noma da cibiyar ke samar wa manoman.

Dakta Attanda ya kara da cewa, wannan aiki ne da cibiyar ta saba gudanar wa duk shekara, muna kuma kiran aikin a matsayin yin nazari dangane da irin binciken da cibiyar ta gudanar a fannin aikin noma, musamman domin mu ji ra’ayoyin manoman a kan irin noman ga cibiyar ta samar.

“Cibiyar ta gudanar da hakan ne domin jin ta bakin manoman a kan ingancin irin noma da cibiyar ke samar wa manoman”.

A na sa jawabin, shugaba kungiyar bunkasa noman mknoma ta kasa reashen jihar Oyo (ADFA) Alhaji Salihu Imam ya yaba wa cibiyar ta NIHORT kan taimaka wa manoma, inda ya yi ikirarin cewa, cibiyar ce kadai, da ta samar wa da manoman da kadada daga 30 zuwa 40 don yin noma ba tare da biyan wani kudin hayar gona ba.

“Cibiyar ce kadai, da ta samar wa da manoman da kadada daga 30 zuwa 40 don yin noma ba tare da biyan wani kudin hayar gona ba”.

Ita ma jami’ar shirin na JDPC ta reshen garin Ibadan, uwargida Adebola Ojewale, wacce kuma tana daya daga cikin wadanda suka amfana ta nuna jin dadinta akan amfanar da suke yi da cibiyar.

Adebola Ojewale ta sanar da cewa,” Na ji dadi matuka domin ko a kwanan baya, manoma na sayo irin noman ne a kasuwanni wadanda akasarin irin, ba shi da ingancin da ake bukata, amma ina da yakinin ganin cewa wamnan irin ya fito ne daga cibiyar, ba ni da wata tantama a kansa”.

Tags: IyakaMinistaNomaShinkafa
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Fitar Da Sabon Bayani Kan Murar Tsintsaye

Next Post

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

Related

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani
Noma Da Kiwo

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

2 hours ago
Kashu
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Samun Fiye Da Dala Miliyan 250 Daga Kashun Da Ake Fitarwa Waje -Minista

1 day ago
Noman Kankana Na Kara Bunkasa A Jihar Jigawa
Noma Da Kiwo

Noman Kankana Na Kara Bunkasa A Jihar Jigawa

1 week ago
Daga 2016 Zuwa 2020, An Kashe Dala Biliyan 6 Wajen Shigo Da Alkama -CBN
Noma Da Kiwo

Daga 2016 Zuwa 2020, An Kashe Dala Biliyan 6 Wajen Shigo Da Alkama -CBN

1 week ago
Yadda Taron Ranar Manoma Ya Gudana A Katsina
Noma Da Kiwo

Yadda Taron Ranar Manoma Ya Gudana A Katsina

2 weeks ago
Gobara Ta Jawo Wa Manoma Asarar Biliyoyin Naira A Ogun
Noma Da Kiwo

Gobara Ta Jawo Wa Manoma Asarar Biliyoyin Naira A Ogun

2 weeks ago
Next Post
Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

February 5, 2023
Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

February 5, 2023
Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

February 5, 2023
Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

February 5, 2023
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

February 5, 2023
Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

February 5, 2023
An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

February 5, 2023
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

February 5, 2023
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

February 5, 2023
Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

February 5, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.