ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

by Abubakar Abba
4 years ago
Abinci

Ministan ma’aikatar noma da raya karkara Dakta Mohammed Mahmood Abubakar ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya na aiki da hukumar yaki da fasakwari domin a dakile shigo da abinci daga kasashen ketare zuwa cikin kasar nan.

Dakta Mohammed ya sanar da hakan ne a jawabinsa yayin ziyarar aiki da ya kai a shalkwatar cibiyar binciken ‘ya’yan itatuwa (NIHORT) da ke garin Ibadan cikin jihar Oyo.

  • Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe
  • Abokai Na Zahiri Suna Zurfafa Huldar Zumunci A Sabon Zamani

A cewar Dakta Mohammed, a cikin shirye-shiyen da gwamnatin tarayya ke kan yi domin ta tabbatar Nijeriya ba ta fuskanci karancin abinci ba, ma’aikarar ta fara shirin fara gudanar da aikin noman rani wanda za a fara a cikin wata mai zuwa, inda ya yi nuni da cewa, fannin aikin noma shi ne na daya da ke kara habaka fannin tattalin arzikiin kasar nan.

ADVERTISEMENT

A cewar Dakta Mohammed,“Zamu tabbatar daukacin hukumomin gwamnati na yin aiki kafada da kafada da hukumar kwastam da muke yin aiki da su, kamar hukumar kwastam domin a tabbatar ba a shigo da abinci ta barauniyar hanya zuwa cikin kasar nan ba domin ba ma son mu samu karancin abinci a kasar nan, inda ya kara da cewa, a yanzu ba ma karancin abinci a kasar nan, muna da wadataccen abinci.

Ministan ya sanar da cewa, shugaban kasa Muhammadu Buhari na bai wa ma’aikatar taimakon da ya dace, domin yana taimaka wa fannin aikin noma ta bayar da gagarumar gudunmowa wajen kara bunkasa tattalin arzikin Nijeriya, inda kuma ya bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa, gwamnatin tarayya za ta ci gaba kara kara bayar da gudunmawa domin cibiyar ta kara fadada gudanar da binciken don a kara bunkasa fannin oma a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

“A yanzu ba ma karancin abinci a kasar nan, muna da wadataccen abinci a kasar nan”.

A taron, Dakta Mohammed ya kuma mika ingantacen irin Kubewa da cibiyar ta NIHORT ta samar gaingantaccen ga sashen bunkasa aikin noma (ADPs) da kuma ga wakilin kungiyoyi masu zaman kansu dake suka fito daga jihohin Oyo, Osun da Ogun.

A na sa jawabin tunda farko, shugaban cibiyar NIHORT Dakta Muhammed Attanda ya godewa ministan, musamman bisa taimakon da cibiyar ke ci gaba da samu daga ma’aikatar noma, inda ya ce, cibiyar ta gudanar da hakan ne domin jin ta bakin manoman a kan irin ingancin irin noma da cibiyar ke samar wa manoman.

Dakta Attanda ya kara da cewa, wannan aiki ne da cibiyar ta saba gudanar wa duk shekara, muna kuma kiran aikin a matsayin yin nazari dangane da irin binciken da cibiyar ta gudanar a fannin aikin noma, musamman domin mu ji ra’ayoyin manoman a kan irin noman ga cibiyar ta samar.

“Cibiyar ta gudanar da hakan ne domin jin ta bakin manoman a kan ingancin irin noma da cibiyar ke samar wa manoman”.

A na sa jawabin, shugaba kungiyar bunkasa noman mknoma ta kasa reashen jihar Oyo (ADFA) Alhaji Salihu Imam ya yaba wa cibiyar ta NIHORT kan taimaka wa manoma, inda ya yi ikirarin cewa, cibiyar ce kadai, da ta samar wa da manoman da kadada daga 30 zuwa 40 don yin noma ba tare da biyan wani kudin hayar gona ba.

“Cibiyar ce kadai, da ta samar wa da manoman da kadada daga 30 zuwa 40 don yin noma ba tare da biyan wani kudin hayar gona ba”.

Ita ma jami’ar shirin na JDPC ta reshen garin Ibadan, uwargida Adebola Ojewale, wacce kuma tana daya daga cikin wadanda suka amfana ta nuna jin dadinta akan amfanar da suke yi da cibiyar.

Adebola Ojewale ta sanar da cewa,” Na ji dadi matuka domin ko a kwanan baya, manoma na sayo irin noman ne a kasuwanni wadanda akasarin irin, ba shi da ingancin da ake bukata, amma ina da yakinin ganin cewa wamnan irin ya fito ne daga cibiyar, ba ni da wata tantama a kansa”.

Abinci
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.