ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Ci Gaba Da Dakile Shigo Da Abinci Daga Ketare -Ministan Noma

by Abubakar Abba
4 years ago
Abinci

Ministan ma’aikatar noma da raya karkara Dakta Mohammed Mahmood Abubakar ya sanar da cewa, gwamnatin tarayya na aiki da hukumar yaki da fasakwari domin a dakile shigo da abinci daga kasashen ketare zuwa cikin kasar nan.

Dakta Mohammed ya sanar da hakan ne a jawabinsa yayin ziyarar aiki da ya kai a shalkwatar cibiyar binciken ‘ya’yan itatuwa (NIHORT) da ke garin Ibadan cikin jihar Oyo.

  • Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe
  • Abokai Na Zahiri Suna Zurfafa Huldar Zumunci A Sabon Zamani

A cewar Dakta Mohammed, a cikin shirye-shiyen da gwamnatin tarayya ke kan yi domin ta tabbatar Nijeriya ba ta fuskanci karancin abinci ba, ma’aikarar ta fara shirin fara gudanar da aikin noman rani wanda za a fara a cikin wata mai zuwa, inda ya yi nuni da cewa, fannin aikin noma shi ne na daya da ke kara habaka fannin tattalin arzikiin kasar nan.

ADVERTISEMENT

A cewar Dakta Mohammed,“Zamu tabbatar daukacin hukumomin gwamnati na yin aiki kafada da kafada da hukumar kwastam da muke yin aiki da su, kamar hukumar kwastam domin a tabbatar ba a shigo da abinci ta barauniyar hanya zuwa cikin kasar nan ba domin ba ma son mu samu karancin abinci a kasar nan, inda ya kara da cewa, a yanzu ba ma karancin abinci a kasar nan, muna da wadataccen abinci.

Ministan ya sanar da cewa, shugaban kasa Muhammadu Buhari na bai wa ma’aikatar taimakon da ya dace, domin yana taimaka wa fannin aikin noma ta bayar da gagarumar gudunmowa wajen kara bunkasa tattalin arzikin Nijeriya, inda kuma ya bai wa ‘yan Nijeriya tabbacin cewa, gwamnatin tarayya za ta ci gaba kara kara bayar da gudunmawa domin cibiyar ta kara fadada gudanar da binciken don a kara bunkasa fannin oma a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

“A yanzu ba ma karancin abinci a kasar nan, muna da wadataccen abinci a kasar nan”.

A taron, Dakta Mohammed ya kuma mika ingantacen irin Kubewa da cibiyar ta NIHORT ta samar gaingantaccen ga sashen bunkasa aikin noma (ADPs) da kuma ga wakilin kungiyoyi masu zaman kansu dake suka fito daga jihohin Oyo, Osun da Ogun.

A na sa jawabin tunda farko, shugaban cibiyar NIHORT Dakta Muhammed Attanda ya godewa ministan, musamman bisa taimakon da cibiyar ke ci gaba da samu daga ma’aikatar noma, inda ya ce, cibiyar ta gudanar da hakan ne domin jin ta bakin manoman a kan irin ingancin irin noma da cibiyar ke samar wa manoman.

Dakta Attanda ya kara da cewa, wannan aiki ne da cibiyar ta saba gudanar wa duk shekara, muna kuma kiran aikin a matsayin yin nazari dangane da irin binciken da cibiyar ta gudanar a fannin aikin noma, musamman domin mu ji ra’ayoyin manoman a kan irin noman ga cibiyar ta samar.

“Cibiyar ta gudanar da hakan ne domin jin ta bakin manoman a kan ingancin irin noma da cibiyar ke samar wa manoman”.

A na sa jawabin, shugaba kungiyar bunkasa noman mknoma ta kasa reashen jihar Oyo (ADFA) Alhaji Salihu Imam ya yaba wa cibiyar ta NIHORT kan taimaka wa manoma, inda ya yi ikirarin cewa, cibiyar ce kadai, da ta samar wa da manoman da kadada daga 30 zuwa 40 don yin noma ba tare da biyan wani kudin hayar gona ba.

“Cibiyar ce kadai, da ta samar wa da manoman da kadada daga 30 zuwa 40 don yin noma ba tare da biyan wani kudin hayar gona ba”.

Ita ma jami’ar shirin na JDPC ta reshen garin Ibadan, uwargida Adebola Ojewale, wacce kuma tana daya daga cikin wadanda suka amfana ta nuna jin dadinta akan amfanar da suke yi da cibiyar.

Adebola Ojewale ta sanar da cewa,” Na ji dadi matuka domin ko a kwanan baya, manoma na sayo irin noman ne a kasuwanni wadanda akasarin irin, ba shi da ingancin da ake bukata, amma ina da yakinin ganin cewa wamnan irin ya fito ne daga cibiyar, ba ni da wata tantama a kansa”.

Abinci
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.