• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yansanda 3 Da Wasu A Sakkwato 

by Sadiq
3 years ago
'Yansanda

Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne, a jiya da yamma, sun kai farmaki kauyen ‘Yarbulutu da ke karamar hukumar Sabon Birni a Jihar Sakkwato, inda suka kashe ‘yansanda uku tare da wasu ‘yan kasuwa uku.

Harin ya faru ne da misalin karfe 2:30 na rana a lokacin da shugaban kasa Muhammadu Buhari da ministan tsaro Salihi Magashi ke Sakkwato suna halartar taron shekara-shekara na COAS na 2022.

  • Yankin Arewa Maso Gabashin Nijeriya Na Bukatar Agajin Gaggawa – MDD
  • Fitacciyar Mawakiya Ta Jamhuriyar Nijar Hamsou Garba Ta Rasu

A cewar wani shaidan gani da ido, ‘yan bindigar da suka zo kan babura sun bude wuta kan ‘yan kasuwar da ba su ji ba ba su gani ba a kasuwar mako-mako, lamarin da ya sanya mutane tserewa, inda suka yi kaca-kaca da kasuwar

Jami’an ‘yansandan da ke wani shingen binciken ababen hawa sun garzaya wurin da ‘yan bindigar nan take suka kashe ‘yansanda uku tare da kone wasu motoci guda biyu.

Da yake tabbatar da harin, kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Sakkwato, DSP Sanusi Abubakar, ya ce rundunar ta samu rahoton kuma suna farautar maharan domin fuskantar shari’a.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Wani mazaunin kauyen da lamarin ya faru a kan idonsa ya bayyana damuwarsa kan yadda ‘yan bindiga ke ta’addanci a yankin a kullum ba tare da wata turjiya ba.

Ya ce an dade ana tsare da kananan hukumomin Sabon Birni da Isa da ke gabashin Sakkwato domin karbar kudin fansa daga ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da ke aiki a Zamfara da kuma wani bangare na Jihar Sakkwato.

“Na tabbata wadannan ‘yan bindigar sun fito ne daga Jihar Zamfara kuma yanzu sun koma yankinmu kamar yadda yankin ke da iyaka da jihar a gabas,” in ji ganau.

Idan ba a manta ba a makon jiya ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari tare da kashe mutane shida a wani kauye na karamar hukumar Goronyo a jihar.

Irin wannan al’amari ya faru a farkon shekarar da ta gabata inda wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kashe sama da mutane 40.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Next Post
Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba – Machina

Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba - Machina

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.