• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Nan Kan Bakana Ban Yarda Malami Ya Shiga Siyasa Ba, Amma… – Farfesa Makari

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ina Nan Kan Bakana Ban Yarda Malami Ya Shiga Siyasa Ba, Amma… – Farfesa Makari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban limamin masallacin Abuja, Farfesa Ibrahim Ahmad Makari ya bayyana cewa yana nan kan ra’ayinsa bai yarda malami ya shiga siyasa ba, amma yana so a bambanta abubuwa guda biyu.

“Bana sha’awar malami ya shiga siyasa daban, amma idan ya kasance wannan malamin yana da wasu ilimi na rayuwa wanda ya shahara a kai, idan har ya shiga siyasa to ko ya yi kuskure ba za a danganta wannan kuskuren da addini ba. Abin da ake nufi dai ilimi ne kadai abin da ake bukata.”

  • Zan Bayyana Dan Takarar Da Zan Mara Wa Baya A Janairu – Wike
  • An Kammala Kashin Farko Na Layin Dogon Jihar Lagos

Farfesa Makari ya kara da cewa akwai hakkin shugaba a kan talakawa, haka kuma akwai hakkin talakawa a kan shugaba wanda suka hada da biyyaya da kuma adalci.

Ya ce wannan zabe da za a gudanar shaida ce da Allah zai taimaya a kai ranar Lahira. Ya ce duk wanda ka zaba kar ka dauka abin wasa, kamar yadda ake raba wa mutane kudi ko omo domin su zabi mutum. A cewarsa, wannan kudi ko omo da aka ba ka domin yin zabe, ka tabbatar da cewa shaida ce wanda Allah zai tambaye ka a ranar tashin kiya.

Farfasa Makari ya shawarci mutane su duba wadanda suka fi yi musu zaton alkairi kamar yin adalci, tausaya wa al’umma, to ka gina zabenka a kan wannan turbali na zaben shugaba. Ya ce lallai mutane su duba wanda zai fi yi wa al’umma abubuwan da suka kamata a zaben shugaba domin su, sai ka yi kokarin gina zabenka a kan wannan ma’auni, amma duk lokacin da al’umma suka makantar da idanuwansu da hankulansu suka gina zabensu kan yadda mutane ke dibar miliyoyin kudade suna wazawa domin a zabesu har su hau wasu mukamai a kan su magance matsaloli, to lallai ba a shirya ganin lokacin magance matsalilin ba.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Ya ce ba zai taba iya fahimtar kishin kasa da za ta sa mutum ya dunga kwaso kudi yana kokarin sayan kujerar da zai yi wa al’umma aiki a kanta ba.

“Ni dai a fahimtata na kasa gane wannan kishin kasa wanda mutum zai kwaso kudi yana rabawa domin ya sayi kujerar da zai yi wa al’umma aiki a kanta.”

Farfasa Makari ya ce, “Akwai kalubale mai girma a gabanmu, abun da ake fadi na cewa ko ka zaba ko baka zaba ba za a zaben maka, wannan magana ba gaskiya ba ce. Lallai wanda zai shugabanci al’umma, yanke hukunci na karshe yana hannun al’umma ne wanda suka bi layi domin zaban wanda zai shugabance su.

“Kaurace wa zabe, mutum ya ce ba zai yi zabe ba saboda wasu dalilai, to zai iya zama kara taimakon masu barna a kan barnar. Saboda ko ka yi zabe ko ba ka yi ba a ranar da za a rantsar da shugaba dole ne a rantsar da shi. Domin rashin zaben ka ba zai sa a kasa rantar da wanda za a rantsar ba.

“Saboda haka, ‘yan’uwa mu yi kokari mu zabi cancanta. Ka da mu mayar da kanmu koma-bayan da wani ya ce mana ku zabi wane, domin muna da hankular kanmu. Sannan kar mu gina zabenmu a kan jam’iyya, dama a farkon maganana na fadi cewa damokuradiyyar nan iya kokarinta take yi ta yi abin da yake daidai, amma karka dauka komi nata daidai ne.

“Idan mutum ya ce maka jam’iyya kaza za ka zaba daga sama har kasa domin ra’ayinsa wanda ba ita ce daidai ba, kai kuma ka duba cancata. Ya kamata mu gane babu wata jam’iyya a yanzu, domin ‘yan takara nawa ne suka sauya sheka wanda har wurin kamfen suna kuskuran iya fadin jam’iyyarsu, saboda sabawa wanda ya kasance jiya suke can, yanzu kuma suna nan, wanda hakan ne ya sa suke kuskuren fadin sunan jam’iyyunsu.

“Bai kamata ana ci gaba da yawo da hankalinmu ba, ya kamata mu yi kokarin gina zabenmu a kan wadanda suka cancanta,” in ji Farfasa Makari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Farfesa MakariMalamiSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Ranakun Hutun Bukukuwan Kirsimeti Da Sabuwar Shekara

Next Post

“Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana’a Ba A Bauchi” —Sadique

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
“Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana’a Ba A Bauchi” —Sadique

“Ba Zamu Raba Wa Mata Da Matasa Akuyoyi Da Sunan Tallafin Sana'a Ba A Bauchi" —Sadique

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.