ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Sace Yara ‘Yan Makaranta 6 A Nasarawa 

by Sadiq
3 years ago
Yara

An samu rudani a unguwar Alwaza da ke karamar hukumar Doma a Jihar Nasarawa, yayin da aka yi garkuwa da yara ‘yan makaranta akalla shida a makarantar firamare a ranar Juma’a.

Hakan dai na zuwa ne kamar yadda rundunar ‘yansandan jihar, ta ce an sace dalibai biyu ne kawai a kan hanyarsu ta zuwa makaranta, ba dalibai shida ba.

  • Dimokuradiyya Ta Zauna Daram A Nijeriya, Ba Batun Juyin Mulki – Shugaban Tsaro
  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

Wata majiya a unguwar da ta nemi a sakaya sunanta ta shaida wa wakilinmu cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 7:00 na safe a lokacin da sauran daliban makarantar ke ci gaba da zuwa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Ba mu taba tsammanin faruwar irin wannan abu a cikin al’ummarmu ba.

“Yaran ‘yan makarantar, kimanin shida daga cikinsu, ‘yan bindiga dauke da muggan makamai ne suka yi garkuwa da su, inda suka tafi da su inda ba a sani ba.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

“A matsayinmu na mazauna unguwar, ba za mu iya yin wani abu don kubutar da su ba, saboda masu laifin suna da makamai amma mun sanar da ‘yansanda halin da ake ciki kuma na yi imanin cewa za su yi kokarin kubutar da daliban da aka sace.”

A halin da ake ciki, kakakin rundunar ‘yansandan jihar, DSP Ramhan Nansel, ya karyata ikirarin cewa an yi garkuwa da wasu daliban makarantar firamaren na, Alwaza, a harabar makarantar.

Ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun sace dalibai biyu ne kawai.

Ya ce sun hada da yara maza biyu ‘yan shekara bakwai zuwa takwas, inda suka kara da cewa suna kan hanyarsu ta zuwa makaranta ne lokacin da lamarin ya faru.

Sai dai kakakin, ya ce ‘yansanda suna samu labarin, kwamishinan ‘yansandan, Maiyaki Baba, ya jagoranci jami’an rundunar, da kungiyoyin ‘yan banga da sauran jami’an tsaro zuwa wurin da harin ya faru.

Ya ce, “Bayanan da nake samu sun ce an dauke yaran maza biyu masu shekaru daga tsakanin bakwai zuwa takwas a hanyarsu ta zuwa makaranta a makarantar firamare ta kauyen Alwaza.

“Da samun bayanan da misalin karfe 7:10 na safiyar yau, tawagar hadin guiwa karkashin jagorancin kwamishinan ‘yansanda da suka hada da ‘yansanda, sojoji da ‘yan banga suka tattaru zuwa wurin da harin ya faru domin kubutar da daliban da aka yi garkuwa da su tare da bankado wadanda wuka aikata laifin.

“Har yanzu muna kokarin gano ‘yan bindigar kuma mun yi alkawarin yin duk abin da za mu iya don magance lamarin.”

Ya yi kira ga mazauna yankin Alwaza da su ci gaba da gudanar da sana’o’insu ba tare da wata fargaba ba.

Kakakin ya yi kira da su kai rahoton duk wata fuska da ba a saba gani ba a yankin ba ga ofishin ‘yansanda mafi kusa da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Mataimakin Shugaban Bankin Duniya: Tattalin Arzikin Sin Zai Kara Bunkasa A Bana

Mataimakin Shugaban Bankin Duniya: Tattalin Arzikin Sin Zai Kara Bunkasa A Bana

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.