• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar LP Ta Kori Dan Takarar Gwamnanta Na Kano, Bashir I. Bashir Daga Jam’iyyar 

by Sadiq
3 years ago
Jam'iyyar LP

Jam’iyyar LP a Jihar Kano, ta yi watsi da ikirarin cewa Bashir Ishak Bashir, wanda ya koma jam’iyyar APC ne dan takararta na gwamna a Jihar.

A ranar Litinin din da ta gabata ne Ishak-Bashir ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai (NAN) cewa ya fara tattaunawa da jam’iyyar APC domin mara mata baya a zabe mai zuwa.

  • ‘Yansanda Sun Ceto Masu Yi Wa Kasa Hidima 15 Da Aka Sace A Anambra
  •  Tsoffin Kudi: Kotun Koli Ta Dage Sauraren Shari’ar Zuwa 22 Ga Fabrairu

“Ina tattaunawa da shugabannin jam’iyyar APC a matakin kasa kan yadda za mu mara wa jam’iyyar baya ta lashe zabe mai zuwa.

Ishak-Bashir ya shaida wa NAN cewa: “Ba da jimawa ba zan tuntube ku kan matsayarmu ta karshe kan lamarin. Shugaban jam’iyyar LP a jihar, Alhaji Mohammed Raji, ya yi watsi da ikirarin Ishak-Bashir, inda ya bayyana cewa ba shi ne dan takarar gwamnan LP a jihar ba.

Raji ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai a ranar Litinin a Kano cewa, sunan Ishak-Bashir bai taba shiga jadawalin Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ba a matsayin dan takarar gwamna na LP a Jihar Kano.

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

“Ya zo jam’iyyar shi kadai ya bar jam’iyyar ba tare da kowa ba,” in ji Raji.

Ya kara da cewa tsarin jam’iyyar ya ci gaba da kasancewa tare da dukkan ‘yan takararta na Sanata, Wakilai da na Majalisar Jiha da ke takara a babban zabe mai zuwa.

Sai dai ya ce akwai batutuwa a cikin jam’iyyar da suka haifar da rashin hadin kai a cikin manyan mukamai da mambobin jam’iyyar.

Raji ya kara da cewa “Wasu abubuwan da ba daidai ba” sun yi kokarin karkatar da hankalin jam’iyyar tare da yin barazanar sauya sheka.

“Muna ba da shawara sosai ga irin wadannan nau’ikan mutane da su sani cewa mu ‘Masu biyayya’ muna goyon bayan takarar Obi da Dati dari bisa dari a Jihar Kano,” in ji shi.

A halin da ake ciki, wata majiya a jam’iyyar ta ce an mika sunan Raji ga INEC a matsayin dan takarar gwamna na LP a Jihar Kano.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
Canjin Kudi: Buhari Ya Yi Ganawar Sirri Da Emefiele

Kin Bin Umarnin Kotu Kan Batun Canjin Kudi Zai Iya Kawo Koma Baya - Masana

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.