• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar LP Ta Kori Dan Takarar Gwamnanta Na Kano, Bashir I. Bashir Daga Jam’iyyar 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Jam’iyyar LP Ta Kori Dan Takarar Gwamnanta Na Kano, Bashir I. Bashir Daga Jam’iyyar 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar LP a Jihar Kano, ta yi watsi da ikirarin cewa Bashir Ishak Bashir, wanda ya koma jam’iyyar APC ne dan takararta na gwamna a Jihar.

A ranar Litinin din da ta gabata ne Ishak-Bashir ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai (NAN) cewa ya fara tattaunawa da jam’iyyar APC domin mara mata baya a zabe mai zuwa.

  • ‘Yansanda Sun Ceto Masu Yi Wa Kasa Hidima 15 Da Aka Sace A Anambra
  •  Tsoffin Kudi: Kotun Koli Ta Dage Sauraren Shari’ar Zuwa 22 Ga Fabrairu

“Ina tattaunawa da shugabannin jam’iyyar APC a matakin kasa kan yadda za mu mara wa jam’iyyar baya ta lashe zabe mai zuwa.

Ishak-Bashir ya shaida wa NAN cewa: “Ba da jimawa ba zan tuntube ku kan matsayarmu ta karshe kan lamarin. Shugaban jam’iyyar LP a jihar, Alhaji Mohammed Raji, ya yi watsi da ikirarin Ishak-Bashir, inda ya bayyana cewa ba shi ne dan takarar gwamnan LP a jihar ba.

Raji ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai a ranar Litinin a Kano cewa, sunan Ishak-Bashir bai taba shiga jadawalin Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ba a matsayin dan takarar gwamna na LP a Jihar Kano.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

“Ya zo jam’iyyar shi kadai ya bar jam’iyyar ba tare da kowa ba,” in ji Raji.

Ya kara da cewa tsarin jam’iyyar ya ci gaba da kasancewa tare da dukkan ‘yan takararta na Sanata, Wakilai da na Majalisar Jiha da ke takara a babban zabe mai zuwa.

Sai dai ya ce akwai batutuwa a cikin jam’iyyar da suka haifar da rashin hadin kai a cikin manyan mukamai da mambobin jam’iyyar.

Raji ya kara da cewa “Wasu abubuwan da ba daidai ba” sun yi kokarin karkatar da hankalin jam’iyyar tare da yin barazanar sauya sheka.

“Muna ba da shawara sosai ga irin wadannan nau’ikan mutane da su sani cewa mu ‘Masu biyayya’ muna goyon bayan takarar Obi da Dati dari bisa dari a Jihar Kano,” in ji shi.

A halin da ake ciki, wata majiya a jam’iyyar ta ce an mika sunan Raji ga INEC a matsayin dan takarar gwamna na LP a Jihar Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBashir I BashirJam'iyyar LPkanoRajaSauya Shekatakara
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Ceto Masu Yi Wa Kasa Hidima 15 Da Aka Sace A Anambra

Next Post

Kin Bin Umarnin Kotu Kan Batun Canjin Kudi Zai Iya Kawo Koma Baya – Masana

Related

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

2 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

15 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

1 day ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

1 day ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

1 day ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
Next Post
Canjin Kudi: Buhari Ya Yi Ganawar Sirri Da Emefiele

Kin Bin Umarnin Kotu Kan Batun Canjin Kudi Zai Iya Kawo Koma Baya - Masana

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.