• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kin Bin Umarnin Kotu Kan Batun Canjin Kudi Zai Iya Kawo Koma Baya – Masana

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Canjin Kudi: Buhari Ya Yi Ganawar Sirri Da Emefiele
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu ruwa da tsaki na gargadi kan rudanin da ka iya biyo bayan watsi da umarnin tsawaita lokacin cikar wa’adin daina amfani da tsoffin takardun Naira.

Biyo bayan kalaman Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, wanda ya ce wa’adin ranar 10 ga watan Fabrairu na daina amfani da tsoffin takardun kudi na Naira 200, 500 da 1000 na nan daram.

  • NUC Ta Daga Darajar Kwalejin Ilimi Ta Sa’adatu Zuwa Jami’ar Ilimi Ta Kano
  • 2023: Duka Ma’aikatan Wucin Gadi Sai Sun Yi Rantsuwar Yin Adalci Ga Kowacce Jam’iyya – INEC

Sai dai masana shari’a da sauran masu ruwa da tsaki a kasar nan sun ce kin bin umarnin kotu da ya bai wa ‘yan kasa damar su ci gaba da amfani da tsoffin takardun kudin har sai kotun ta yanke hukunci a kan lamarin, zai iya kawo yamutsi a kasar nan.

Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, ya bayyana wannan matsaya na babu gudu ba ja da baya a game da daina amafani da tsoffin takardun kudin ne a lokacin da yake zantawa da jami’an diflomasiyya a Ma’aikatar Harkokin Waje da ke birnin Tarayya Abuja a ranar Talata.

Emefiele ya ce an fara samun sauki a al’amarin karancin sabbin takardun kudi sosai tun lokacin da aka fara biyan kudaden a cikin bankuna wato baya ga samu a nau’urar ATM da kuma amfani da manyan wakilan CBN, yana mai cewa don haka babu bukatar yin la’akari da wani sauyi daga wa’adin ranar 10 ga Fabrairu.

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

HaÉ—akar Jam’iyyun Adawa Ba Ya ÆŠaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Bayanin na Emefiele na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan kasa ke cikin rudani a game da umarnin kotun kolin da ta tsawaita wa’adin zuwa ranar 15 ga watan Fabrairu har zuwa ga lokacin da kotun za ta yi sauraren karar da gwamnonin uku daga Arewacin kasar nan suka shigar a gabanta.

Shin mene ne tanadin doka idan aka samu irin wannan sabani da ake gani inda bankin CBN ya ce ba zai sauya matsaya ba duk da umarnin kotun koli, Barrista Mainasa Kogo, a zantawarsa da VOA Hausa, ya ce kememe da gwamna Emefiele ya yi da kuma kin bin umarnin kotu zai iya kawo yamutsi a kasa kasancewa al’umma na cikin halin kakani-kayi.

Mai sharhi a kan al’amuran yau da kullum, Mal. Baba Yusuf, ya bayyana cewa kememe da gwamna Emefiele ya yi ba laifinsa ba ne illa ‘yan Nijeriya su jira matsayin da shugaba Muhammadu Buhari zai dauka, inda ya yi kira da a duba halin ha’ula’i da ‘yan kasa ke ciki don saukaka musu wahalhalu da suka sha.

Ko yaya ‘yan kasa ke ganin wannan al’amari, Malam Ibrahim mai kantin sayar da kayayyakin amfani na yau da kullum ya ce suna cikin mawuyacin hali.

Wannan lamari dai ya haifar da zanga-zanga a wasu jihohin kasar nan, a wasu yankuna kuma gwamnatocin jihohi ne suka yo barazana ga duk wanda ya ki karbar tsofaffin takardun kudin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariCanjin KudiCBNEmefieleKotuMasana
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jam’iyyar LP Ta Kori Dan Takarar Gwamnanta Na Kano, Bashir I. Bashir Daga Jam’iyyar 

Next Post

Abin Da Ya Sa Muka Tsare Fani-Kayode -DSS

Related

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

2 hours ago
HaÉ—akar Jam’iyyun Adawa Ba Ya ÆŠaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

HaÉ—akar Jam’iyyun Adawa Ba Ya ÆŠaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

3 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

13 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

16 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

1 day ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

1 day ago
Next Post
Abin Da Ya Sa Muka Tsare Fani-Kayode -DSS

Abin Da Ya Sa Muka Tsare Fani-Kayode -DSS

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
HaÉ—akar Jam’iyyun Adawa Ba Ya ÆŠaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

HaÉ—akar Jam’iyyun Adawa Ba Ya ÆŠaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.