• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Sake Sallamar Malaman Makaranta 2,357 Daga Aiki

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Kaduna Ta Sake Sallamar Malaman Makaranta 2,357 Daga Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Ilimin Bai Daya ta Jihar Kaduna (KADSUBEB), ta ce ta sallami malaman makaranta 2,357 sakamakon faduwa jarabawar da ta sake shirya musu a kwananakin baya.

Kakakin hukumar, Hauwa Mohammed ce ta sanar da hakan a cikin wata sanarwar da ta fitar a ranar Lahadi.

  • NiMet Ta Yi Hasashen Samun Hadari Da Tsawa Na Kwanaki 3 Daga Ranar Litinin
  • Kwankwaso Ba Zai Yi Wa Peter Obi Takarar Mataimaki Ba — NNPP

Ta ce sun shirya jarabawar ce ga malamai sama da 30,000 a watan Disambar 2021.

A cewarta daga malaman firamare 2,192, ciki har da Shugaban Kungiyar Malamai ta Kasa (NUT), Misis Audu Amba, aka sallama daga aiki saboda kin zana jarabawar.

Ta ce akwai wasu malamai 165 daga cikin 27,662 da suka zana jarabawar da su kuma aka kore su saboda rashin kokari.

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

“Mun gano cewa ba mu da bukatar dukkan malaman da suka samu kasa da kaso 40 cikin 100 na maki a jawabawar, saboda haka mun sallame su daga aiki.

“Malaman kuwa da suka samu kaso 75 cikin 100 su ne muka tantance a matsayin kwararrun malamai da suka cancanta su ci gaba da koyarwa kuma za su fara zuwa kwasa-kwasai kan shugabanci da gudanarwar makarantu,” inji ta.

Da yake mayar da martani kan batun, Shugaban NUT na Jihar, Ibrahim Dalhatu, ya yi watsi da jarawabar da ma korar da aka masa, inda ya bayyana su a matsayin wadanda aka yi ba bisa ka’ida ba.

Sai dai ya ce tuni kungiyarsu ta samu umarnin kotu da ya hana gwamnati shirya jarabawar, amma duk da haka ta yi kunnen uwar shegu da umarnin.

Shi ma da yake maida martani, shugaban NUT na kasa, ya ce suna sane da lamarin, kuma za su zauna ranar Laraba don tattaunawa a kan batun.

A shekarar 2018, gwamnatin jihar ta kori malamai 21,780 da suka fadi jarabawar, sannan ta maye gurbinsu da wasu 25,000.

Har wa yau, a watan Disamban 2021 ta sake sallamar wasu malaman guda 233 saboda amfani da takardun bogi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin KadunaJarabawaKadunaKoraMalaman MakarantaNUTSallama daga Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Hadari Da Tsawa Na Kwanaki 3 Daga Ranar Litinin

Next Post

Tawagar NIS Ta Kai Ziyarar Aiki A Poland Kan Tsaron Iyakoki

Related

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

2 hours ago
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne
Labarai

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

4 hours ago
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

5 hours ago
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Labarai

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

6 hours ago
Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

18 hours ago
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Labarai

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

19 hours ago
Next Post
Tawagar NIS Ta Kai Ziyarar Aiki A Poland Kan Tsaron Iyakoki

Tawagar NIS Ta Kai Ziyarar Aiki A Poland Kan Tsaron Iyakoki

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.