• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shinge 4 Da Sabon Gwamnan Zamfara Ya Tsallake Kafin Ya Doke Matawalle

by Bello Hamza
2 years ago
in Rahotonni
0
Shinge 4 Da Sabon Gwamnan Zamfara Ya Tsallake Kafin Ya Doke Matawalle
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata 21 ga watan Maris 2023 ne al’ummar Nijeriya suka tashi da labarin wata girgiza fagen siyasar kasar nan, inda aka sanar da cewa, dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP Dakta Dauda Lawal Dare, ya lashe zaben da aka yi na gwamna a ranar 18 ga watan Maris 2023 a Jihar Zamfara, inda ya yi waje rod da gwamna mai ci na jam’iyyar APC, Daklta Bello Matawalle.

Jami’in kula da zaben da aka yi, Farfesa Kasimu Shehu, ya sanar da cewa, sakamakon zaben da aka yi ya nuna cewa, Dauda Dare ya samu kuri’a 377,726 inda ya kayar da Matawalle wanda ya tashi da kuri’a 311,976.

  • Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana
  • Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun

Tuni aka barke da murnar wannan nasarar da Lawal na PDP ya samu a sassan jihar Zamfara dama Nijeriya baki daya, nasarar da ake gani lallai ta samu ne ta hanyar jajircewa da aiki tukuru daga Dan takarar Dakta Lawal da bangaren jam’iyyar PDP gaba daya.

Tabbas wannan nasarar ta Dauda Lawal bata zo da sauki ba, ya ci karo da shingaye da dama. Dauda wanda tsohon ma’aikacin Banki ne ya fuskanci shari’u da dama har zuwa makonni kadan kafin a fuskanci zaben, shari’un neman tabbatar da shi a matsayin dan takarar gwamnan Zamfara, amma cikin ikon Allah ya samu nasara a dukkan shari’un da ya fuskanta.

Tun farko a watan Satumba na shekarar 20022, wata kotun tarayya da ke Gusau ta soke takararsa kan cewa, taron da aka yi inda aka zabe shi a mastayin dan takarar ba halastacciya ba ne, wani tsohon dan majalisar tarayya ne mai suna Alhaji Ibrahim Shehu Gusau, ya nemi kotu ta soke zaben, a cewarsa an tafka magudi a zabukkan da aka yi. Maishari’a Aminu Bappa ya soke zaben a ranar 25 ga wata Mayu 2022 inda ya nemi a sake gudanar da wani zaben fidda gwani.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Duk da cewa, Lawal ya sake lashe zaben fidda gwani da aka yi amma kotun ta kuma dakatar da aiwatar da zaben sa da aka yi.

Haka kuma Maishari’a Bappa ya sake soke zaben ya kuma zartar da cewa, jam’iyyar PDP ba za ta iya gabatar da dan takarar a jihar Zamfara a zaben 2023 gaba daya ba.

Amma Lawal bai sadakar ba, inda shi da Adamu Maina-Waziri, shugaban kwamitin da ya gudanar da zaben fidda gwamni Kanal Bala Mande (mai Ritaya) suka daukaka kara a babban kotun daukaka kara na Sakwatto inda suka nemi kotu da soke umarnin.

A watan Janairu na 2023 babbar kotun a karkashin Maishari’a Abubakar Talba, ta yi watsi da hukunci inda ta sake amincewa da Dakta Lawal a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP a zaben da za a yi.

Karin shinge

Duk da wadannan nasarorin da Lawal ya samu, sai gashi an daukaka karar zuwa kotun koli. Inda a ranar 6 ga watan Maris 2023, ya sake samun nasarar a kotun koli inda ta zartar da cewa, Lawal ne halastaccen dan takarar jam’iyyar PDP kuma shi ne zai tsaya mata takara a zaben 2023.

Haka kuma Lawal ya fuskanci shari’a daga hukumar EFCC, inda shari’ar ta kai ga kotun koli amma cikin ikon Allah Lawal ya samu cikakken nasara inda kotun ta wanke shi daga dukkan zarge-zarge.

Daga ranar 29 ga watan Mayu na shekarar 2023 Dakta Lawal Dare zai karbi ragamar mulki Jihar Zamfara daga hannun Bello Matawale inda zai cigaba da aiwatar da alkawuran da ya yi wa la’umma, muna fatan al’umma za su bashi dukkan goyon bayan da yake bukata don kai Jihar Zamfa tudun-mun-tsira.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DareMatawalleZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Darussan Da ‘Yan Siyasa Za Su Koya A Zaben 2023

Next Post

Tarihin Mamayar Tattar 4

Related

Zamfara
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

16 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

2 days ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
Tarihin Mamayar Tattar 4

Tarihin Mamayar Tattar 4

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.