• Leadership Hausa
Sunday, June 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Mamayar Tattar 4

by Idris Aliyu Daudawa
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Tarihin Mamayar Tattar 4
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ci gaba daga shafi na makon da ya gabata

Dalillan da Suka Karfafa Yakin Tattar

Tun da farko yana da kyau mu gano dalillan da suka karfafa bayyanar wadannan mahalukai masu kama da aljanu:

  1. Tattar sun tun faro kasar Musulunci a daidai lokacin da al’ummar Musulmi take cikin rauni a kowane bangare. Ga dai rarrabar kawuna wadda Allah ya hana mu. Ga talauci wanda ya faru a sanadiyyar yawan ambaliyar ruwa da aka yi shekaru ana yi wanda ya kawo wahalar abinci da tsadar rayuwa. Ga kuma ‘yan rigingimu da aka yi ta yi tsakanin Ahlus-Sunnah da tsirarun ‘yan Shi’ar da waziri ya daure masu gindi. Ga kuma karancin soja wadanda waziri ya kokkore su daga aiki yana nuna ma halifa cewa, akwai bukatar kula da tattalin arziki, don haka bai kamata a kashe kudaden gwamnati a kan soji ba.
  2. Halifan daular Abbasiyya na wancan lokaci mutumin kirki ne, mai son addini amma ba shi da ikon kome a hannunsa in ban da a birnin Bagadaza. Halifa kawai ya zama wani dodo wanda ba a ko iya ganin sa. An rufe shi cikin gida daga shi sai barori da

kuyangi. Bai san abin da duniya take ciki ba, kuma ita ma duniyar ba ta san abin da yake ciki ba.

  1. Kananan daulolin musulunci sun yarda da shugabancin Bagadaza kamar daular Ayubawa da ta Gaznawa da ta Khuwarizmawa da duk sauran kananan daulolin Musulunci in ban da daular ‘yan Shi’a ta Masar da ta Sufaye a Moroko. Su kam ba su

ma amince da halifa ba. Amma duka wadannan daulolin tare da amincewar su da gwamnatin Sunnah ta Bagadaza ba su zaune lafiya da ita. An yi ta yake- yake wadanda suka raunana kowane bangare.

Labarai Masu Nasaba

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

Akwai wata dirama da ta faru a shekarar 529H a lokacin da sarki Mahmud ya yi yunkurin juyin mulki a kan Halifa Mustarshid, ya kuma ci nasara har da kama Halifa a hannu. Daga bisani kuma sarki “Sabjar” ya shiga tsakani bayan wani bore da

talakawa suka yi, ya sasanta har aka mayar da halifa a kan kujerarsa. Shekara daya bayan haka sai kuma sarki Mas’udu ya bayyana nasa tawayen, ya shelanta ya cire halifa ya nada kanin babansa Al- Muktafi, haka din kuma aka yi.

Bayan shekaru 11 aka samu wani rikici tsakanin halifa Muktafi da mai gidansa abinda ya jawo halifan ya sa aka rufe dukkan masallatai har tsawon kwana 3 ba a sallah cikin su. Bayan wasu shekaru 10 kuma aka sake wani ya mutsi tsakanin halifa da sarki Muhammad dan sarki Mahmud abin da ya jawo aka yi wata 2 ana zaman dar-dar a Bagadaza.

A takaice dai koda Tattar suka zo ba wani sarki da yake da karfi ko yake da cikakken hadin kai da wani in ban da Khuwarizm Shah. Don haka da gamawa da shi sai fili ya koma wayam; ba mai iya jayayya da su.

  1. A daidai lokacin da Musulmi suke cikin wannan rauni, sarakuna suka shagala da wasanni da sabon Allah, su kuma rundunar Tattar runduna ce kammalalliya. Duk inda suka zo basu bukatar kowa ya ba su ko igiyar daure rakumi. Suna da da wakai da

ra kuma da shanu wadanda suke cin namansu, da wadanda suke hawa kuma ba su bukatar a sauya masu dusa ko a ajiye masu kasari ko wani abinci, tonon kasa suke suna cin kwari da ciyawa da duk abin da ya samu. Ga su da yawan adadi wanda

mahaliccinmu kadai ya san iyakarsa. Ba su da tsoro, ba su ja da baya, ba su da jin kai ko miskala-zarratin ga mutane.

  1. Akwai wasu kura kurai da gangancin da sarakunan Musulunci suka yi musamman ma dai Khuwarizm Shah lokacin da ya kashe wasu ‘yan kasuwa da suka zo daga kasar Sin ba bisa ga wani dalili ba kuma ya kwace masu dukiya. A lokacin da wannan labari ya je ga Jinkizkhan sai ya aika masa wasika yana barazanar zai dau fansa, sai kuma Khuwarizmshah ya kashe jakadan ya sa aka aske gemun ‘yan rakiyarsa ya ce musu su je su kai labari.

Daga nan kuma sarki Khuwarizmshah ya je don yakar Tattar ya tarar sun fita zuwa Turkiyya don yaki da wani sarki ana ce masa Kashlokhan. Khuwarizm ya shiga garinsu, ya auka ma matansu da ‘ya’yansu amma bai bar garin ba sai da suka cim ma sa suka gwabza yaki mai tsanani. A cikin kwanaki uku suka kashe masa jarumawa Musulmi 20,000.

Tare da haka su ma sun yi hasarar rayuka ba iyaka. Tarihi ya ruwaito cewa, saboda yawan jinin da ya zuba na jama’a har zamewa dawa kai ke yi a cikinsa. 6. Kiristoci wadanda suka kasa karya lagon Musulmi a yakin Kuros (Crusade) ‘yan shekaru kadan a baya su ma sun taka rawa wajen kwadaitar da Tattar a kan kama kasashen Musulmi. Suka rinka nuna masu irin arzikin da ke cikin kasashen da saukin cin galaba a kansu.

A lokacin da Tattar suka kama kasashen Sham sun bayyana goyon bayansu ga kiristoci har su kan sa Musulmi su duka ma Kuros don wulakanta su.

  1. Akwai kuma tasirin munafukan Musulmi, ina nufin ‘yan Shi’ah. Tun a zamanin sarki Nasir dan sarki Mustadi’u bi amrillah wanda ya fi duk sarakunan daular Abbasiyyah dadewa (ya yi sarauta shekaru 47 daga 575H-622H) shi’anci ya fara karfi a cikin daular Musulunci saboda kisisinar da ‘yan Shi’ah suka yi ma sarki na aiko masa da takarda a sirrance rubuce da duk abin da ya yi a cikin dare, shi kuma sai ya yi tsammanin gaskiya ne Imaman Shi’ah sun sai gaibi kuma su ne ke fada masu sirrinsa. Alhalin kuwa yan leken asiri gare su daga cikin barorinsa. Wannan sarki – saboda shi’ancinsa – ya yi ta nuna ma Tattar goyon baya da ba su asirran Musulmi.

A kodayaushe yana aika masu wasiku. Sai na biyu shi ne sarkin garin Musil wanda ake ma lakabi da Al-Malik Ar- Rahim. Wannan sarki shi ma ya dade yana sarauta (tsawon shekaru 50), kuma dan Shi’ah ne da ya raya wasu al’adu da bukukuwa na kiristoci, ya kuma kulla alaka mai karfi da Tattar har da aurar da dansa Salihu ga ‘yar sarkin Tattar na wancan lokaci Hulako, duk da yake auren bai yi karko ba kuma ya haifar da rashin jituwa a tsakanin su amma dai ya ba da goyon baya da gudunmawa ga Tattar har ma mayakansa sun taimaka wajen yakar Bagadaza. Na uku shi ne uwa uba ga wannan al’amari, ina nufin Waziri Mu’ayyiduddin Muhammad Ibnu Ahmad Ibnul Alkami wanda ya hau mukamin waziri a zamanin sarki Musta’asim tsawon shekaru 14. Kuma ya yi iya kokarinsa ya daukaka shi’anci amma Ahlus- Sunnah suka rinjaye shi, sai ya bi ta hanyar hila da makirci kamar yadda muka riga muka fada.

Tags: BukharaTarihi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shinge 4 Da Sabon Gwamnan Zamfara Ya Tsallake Kafin Ya Doke Matawalle

Next Post

Gidan Da Aka Farmaka A Bauchi Ba Na Shugaban INEC Ba Ne – Oyekanmi

Related

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano
Manyan Labarai

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

4 hours ago
Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu
Manyan Labarai

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

10 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

1 day ago
Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano
Manyan Labarai

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

1 day ago
Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

2 days ago
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur
Manyan Labarai

Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

2 days ago
Next Post
Gidan Da Aka Farmaka A Bauchi Ba Na Shugaban INEC Ba Ne – Oyekanmi

Gidan Da Aka Farmaka A Bauchi Ba Na Shugaban INEC Ba Ne - Oyekanmi

LABARAI MASU NASABA

Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

June 4, 2023
Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

June 4, 2023
Sana’ar Kwalliya

Sana’ar Kwalliya

June 4, 2023
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

June 4, 2023
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

June 4, 2023
Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

June 4, 2023
Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

June 4, 2023
Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

June 4, 2023
Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

June 4, 2023
Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

June 3, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.