ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Mamayar Tattar 4

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Tarihin

Ci gaba daga shafi na makon da ya gabata

Dalillan da Suka Karfafa Yakin Tattar

Tun da farko yana da kyau mu gano dalillan da suka karfafa bayyanar wadannan mahalukai masu kama da aljanu:

ADVERTISEMENT
  1. Tattar sun tun faro kasar Musulunci a daidai lokacin da al’ummar Musulmi take cikin rauni a kowane bangare. Ga dai rarrabar kawuna wadda Allah ya hana mu. Ga talauci wanda ya faru a sanadiyyar yawan ambaliyar ruwa da aka yi shekaru ana yi wanda ya kawo wahalar abinci da tsadar rayuwa. Ga kuma ‘yan rigingimu da aka yi ta yi tsakanin Ahlus-Sunnah da tsirarun ‘yan Shi’ar da waziri ya daure masu gindi. Ga kuma karancin soja wadanda waziri ya kokkore su daga aiki yana nuna ma halifa cewa, akwai bukatar kula da tattalin arziki, don haka bai kamata a kashe kudaden gwamnati a kan soji ba.
  2. Halifan daular Abbasiyya na wancan lokaci mutumin kirki ne, mai son addini amma ba shi da ikon kome a hannunsa in ban da a birnin Bagadaza. Halifa kawai ya zama wani dodo wanda ba a ko iya ganin sa. An rufe shi cikin gida daga shi sai barori da

kuyangi. Bai san abin da duniya take ciki ba, kuma ita ma duniyar ba ta san abin da yake ciki ba.

  1. Kananan daulolin musulunci sun yarda da shugabancin Bagadaza kamar daular Ayubawa da ta Gaznawa da ta Khuwarizmawa da duk sauran kananan daulolin Musulunci in ban da daular ‘yan Shi’a ta Masar da ta Sufaye a Moroko. Su kam ba su

ma amince da halifa ba. Amma duka wadannan daulolin tare da amincewar su da gwamnatin Sunnah ta Bagadaza ba su zaune lafiya da ita. An yi ta yake- yake wadanda suka raunana kowane bangare.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Akwai wata dirama da ta faru a shekarar 529H a lokacin da sarki Mahmud ya yi yunkurin juyin mulki a kan Halifa Mustarshid, ya kuma ci nasara har da kama Halifa a hannu. Daga bisani kuma sarki “Sabjar” ya shiga tsakani bayan wani bore da

talakawa suka yi, ya sasanta har aka mayar da halifa a kan kujerarsa. Shekara daya bayan haka sai kuma sarki Mas’udu ya bayyana nasa tawayen, ya shelanta ya cire halifa ya nada kanin babansa Al- Muktafi, haka din kuma aka yi.

Bayan shekaru 11 aka samu wani rikici tsakanin halifa Muktafi da mai gidansa abinda ya jawo halifan ya sa aka rufe dukkan masallatai har tsawon kwana 3 ba a sallah cikin su. Bayan wasu shekaru 10 kuma aka sake wani ya mutsi tsakanin halifa da sarki Muhammad dan sarki Mahmud abin da ya jawo aka yi wata 2 ana zaman dar-dar a Bagadaza.

A takaice dai koda Tattar suka zo ba wani sarki da yake da karfi ko yake da cikakken hadin kai da wani in ban da Khuwarizm Shah. Don haka da gamawa da shi sai fili ya koma wayam; ba mai iya jayayya da su.

  1. A daidai lokacin da Musulmi suke cikin wannan rauni, sarakuna suka shagala da wasanni da sabon Allah, su kuma rundunar Tattar runduna ce kammalalliya. Duk inda suka zo basu bukatar kowa ya ba su ko igiyar daure rakumi. Suna da da wakai da

ra kuma da shanu wadanda suke cin namansu, da wadanda suke hawa kuma ba su bukatar a sauya masu dusa ko a ajiye masu kasari ko wani abinci, tonon kasa suke suna cin kwari da ciyawa da duk abin da ya samu. Ga su da yawan adadi wanda

mahaliccinmu kadai ya san iyakarsa. Ba su da tsoro, ba su ja da baya, ba su da jin kai ko miskala-zarratin ga mutane.

  1. Akwai wasu kura kurai da gangancin da sarakunan Musulunci suka yi musamman ma dai Khuwarizm Shah lokacin da ya kashe wasu ‘yan kasuwa da suka zo daga kasar Sin ba bisa ga wani dalili ba kuma ya kwace masu dukiya. A lokacin da wannan labari ya je ga Jinkizkhan sai ya aika masa wasika yana barazanar zai dau fansa, sai kuma Khuwarizmshah ya kashe jakadan ya sa aka aske gemun ‘yan rakiyarsa ya ce musu su je su kai labari.

Daga nan kuma sarki Khuwarizmshah ya je don yakar Tattar ya tarar sun fita zuwa Turkiyya don yaki da wani sarki ana ce masa Kashlokhan. Khuwarizm ya shiga garinsu, ya auka ma matansu da ‘ya’yansu amma bai bar garin ba sai da suka cim ma sa suka gwabza yaki mai tsanani. A cikin kwanaki uku suka kashe masa jarumawa Musulmi 20,000.

Tare da haka su ma sun yi hasarar rayuka ba iyaka. Tarihi ya ruwaito cewa, saboda yawan jinin da ya zuba na jama’a har zamewa dawa kai ke yi a cikinsa. 6. Kiristoci wadanda suka kasa karya lagon Musulmi a yakin Kuros (Crusade) ‘yan shekaru kadan a baya su ma sun taka rawa wajen kwadaitar da Tattar a kan kama kasashen Musulmi. Suka rinka nuna masu irin arzikin da ke cikin kasashen da saukin cin galaba a kansu.

A lokacin da Tattar suka kama kasashen Sham sun bayyana goyon bayansu ga kiristoci har su kan sa Musulmi su duka ma Kuros don wulakanta su.

  1. Akwai kuma tasirin munafukan Musulmi, ina nufin ‘yan Shi’ah. Tun a zamanin sarki Nasir dan sarki Mustadi’u bi amrillah wanda ya fi duk sarakunan daular Abbasiyyah dadewa (ya yi sarauta shekaru 47 daga 575H-622H) shi’anci ya fara karfi a cikin daular Musulunci saboda kisisinar da ‘yan Shi’ah suka yi ma sarki na aiko masa da takarda a sirrance rubuce da duk abin da ya yi a cikin dare, shi kuma sai ya yi tsammanin gaskiya ne Imaman Shi’ah sun sai gaibi kuma su ne ke fada masu sirrinsa. Alhalin kuwa yan leken asiri gare su daga cikin barorinsa. Wannan sarki – saboda shi’ancinsa – ya yi ta nuna ma Tattar goyon baya da ba su asirran Musulmi.

A kodayaushe yana aika masu wasiku. Sai na biyu shi ne sarkin garin Musil wanda ake ma lakabi da Al-Malik Ar- Rahim. Wannan sarki shi ma ya dade yana sarauta (tsawon shekaru 50), kuma dan Shi’ah ne da ya raya wasu al’adu da bukukuwa na kiristoci, ya kuma kulla alaka mai karfi da Tattar har da aurar da dansa Salihu ga ‘yar sarkin Tattar na wancan lokaci Hulako, duk da yake auren bai yi karko ba kuma ya haifar da rashin jituwa a tsakanin su amma dai ya ba da goyon baya da gudunmawa ga Tattar har ma mayakansa sun taimaka wajen yakar Bagadaza. Na uku shi ne uwa uba ga wannan al’amari, ina nufin Waziri Mu’ayyiduddin Muhammad Ibnu Ahmad Ibnul Alkami wanda ya hau mukamin waziri a zamanin sarki Musta’asim tsawon shekaru 14. Kuma ya yi iya kokarinsa ya daukaka shi’anci amma Ahlus- Sunnah suka rinjaye shi, sai ya bi ta hanyar hila da makirci kamar yadda muka riga muka fada.

Tarihin
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Gidan Da Aka Farmaka A Bauchi Ba Na Shugaban INEC Ba Ne – Oyekanmi

Gidan Da Aka Farmaka A Bauchi Ba Na Shugaban INEC Ba Ne - Oyekanmi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.