ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Mamayar Tattar 4

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Tarihin

Ci gaba daga shafi na makon da ya gabata

Dalillan da Suka Karfafa Yakin Tattar

Tun da farko yana da kyau mu gano dalillan da suka karfafa bayyanar wadannan mahalukai masu kama da aljanu:

ADVERTISEMENT
  1. Tattar sun tun faro kasar Musulunci a daidai lokacin da al’ummar Musulmi take cikin rauni a kowane bangare. Ga dai rarrabar kawuna wadda Allah ya hana mu. Ga talauci wanda ya faru a sanadiyyar yawan ambaliyar ruwa da aka yi shekaru ana yi wanda ya kawo wahalar abinci da tsadar rayuwa. Ga kuma ‘yan rigingimu da aka yi ta yi tsakanin Ahlus-Sunnah da tsirarun ‘yan Shi’ar da waziri ya daure masu gindi. Ga kuma karancin soja wadanda waziri ya kokkore su daga aiki yana nuna ma halifa cewa, akwai bukatar kula da tattalin arziki, don haka bai kamata a kashe kudaden gwamnati a kan soji ba.
  2. Halifan daular Abbasiyya na wancan lokaci mutumin kirki ne, mai son addini amma ba shi da ikon kome a hannunsa in ban da a birnin Bagadaza. Halifa kawai ya zama wani dodo wanda ba a ko iya ganin sa. An rufe shi cikin gida daga shi sai barori da

kuyangi. Bai san abin da duniya take ciki ba, kuma ita ma duniyar ba ta san abin da yake ciki ba.

  1. Kananan daulolin musulunci sun yarda da shugabancin Bagadaza kamar daular Ayubawa da ta Gaznawa da ta Khuwarizmawa da duk sauran kananan daulolin Musulunci in ban da daular ‘yan Shi’a ta Masar da ta Sufaye a Moroko. Su kam ba su

ma amince da halifa ba. Amma duka wadannan daulolin tare da amincewar su da gwamnatin Sunnah ta Bagadaza ba su zaune lafiya da ita. An yi ta yake- yake wadanda suka raunana kowane bangare.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Akwai wata dirama da ta faru a shekarar 529H a lokacin da sarki Mahmud ya yi yunkurin juyin mulki a kan Halifa Mustarshid, ya kuma ci nasara har da kama Halifa a hannu. Daga bisani kuma sarki “Sabjar” ya shiga tsakani bayan wani bore da

talakawa suka yi, ya sasanta har aka mayar da halifa a kan kujerarsa. Shekara daya bayan haka sai kuma sarki Mas’udu ya bayyana nasa tawayen, ya shelanta ya cire halifa ya nada kanin babansa Al- Muktafi, haka din kuma aka yi.

Bayan shekaru 11 aka samu wani rikici tsakanin halifa Muktafi da mai gidansa abinda ya jawo halifan ya sa aka rufe dukkan masallatai har tsawon kwana 3 ba a sallah cikin su. Bayan wasu shekaru 10 kuma aka sake wani ya mutsi tsakanin halifa da sarki Muhammad dan sarki Mahmud abin da ya jawo aka yi wata 2 ana zaman dar-dar a Bagadaza.

A takaice dai koda Tattar suka zo ba wani sarki da yake da karfi ko yake da cikakken hadin kai da wani in ban da Khuwarizm Shah. Don haka da gamawa da shi sai fili ya koma wayam; ba mai iya jayayya da su.

  1. A daidai lokacin da Musulmi suke cikin wannan rauni, sarakuna suka shagala da wasanni da sabon Allah, su kuma rundunar Tattar runduna ce kammalalliya. Duk inda suka zo basu bukatar kowa ya ba su ko igiyar daure rakumi. Suna da da wakai da

ra kuma da shanu wadanda suke cin namansu, da wadanda suke hawa kuma ba su bukatar a sauya masu dusa ko a ajiye masu kasari ko wani abinci, tonon kasa suke suna cin kwari da ciyawa da duk abin da ya samu. Ga su da yawan adadi wanda

mahaliccinmu kadai ya san iyakarsa. Ba su da tsoro, ba su ja da baya, ba su da jin kai ko miskala-zarratin ga mutane.

  1. Akwai wasu kura kurai da gangancin da sarakunan Musulunci suka yi musamman ma dai Khuwarizm Shah lokacin da ya kashe wasu ‘yan kasuwa da suka zo daga kasar Sin ba bisa ga wani dalili ba kuma ya kwace masu dukiya. A lokacin da wannan labari ya je ga Jinkizkhan sai ya aika masa wasika yana barazanar zai dau fansa, sai kuma Khuwarizmshah ya kashe jakadan ya sa aka aske gemun ‘yan rakiyarsa ya ce musu su je su kai labari.

Daga nan kuma sarki Khuwarizmshah ya je don yakar Tattar ya tarar sun fita zuwa Turkiyya don yaki da wani sarki ana ce masa Kashlokhan. Khuwarizm ya shiga garinsu, ya auka ma matansu da ‘ya’yansu amma bai bar garin ba sai da suka cim ma sa suka gwabza yaki mai tsanani. A cikin kwanaki uku suka kashe masa jarumawa Musulmi 20,000.

Tare da haka su ma sun yi hasarar rayuka ba iyaka. Tarihi ya ruwaito cewa, saboda yawan jinin da ya zuba na jama’a har zamewa dawa kai ke yi a cikinsa. 6. Kiristoci wadanda suka kasa karya lagon Musulmi a yakin Kuros (Crusade) ‘yan shekaru kadan a baya su ma sun taka rawa wajen kwadaitar da Tattar a kan kama kasashen Musulmi. Suka rinka nuna masu irin arzikin da ke cikin kasashen da saukin cin galaba a kansu.

A lokacin da Tattar suka kama kasashen Sham sun bayyana goyon bayansu ga kiristoci har su kan sa Musulmi su duka ma Kuros don wulakanta su.

  1. Akwai kuma tasirin munafukan Musulmi, ina nufin ‘yan Shi’ah. Tun a zamanin sarki Nasir dan sarki Mustadi’u bi amrillah wanda ya fi duk sarakunan daular Abbasiyyah dadewa (ya yi sarauta shekaru 47 daga 575H-622H) shi’anci ya fara karfi a cikin daular Musulunci saboda kisisinar da ‘yan Shi’ah suka yi ma sarki na aiko masa da takarda a sirrance rubuce da duk abin da ya yi a cikin dare, shi kuma sai ya yi tsammanin gaskiya ne Imaman Shi’ah sun sai gaibi kuma su ne ke fada masu sirrinsa. Alhalin kuwa yan leken asiri gare su daga cikin barorinsa. Wannan sarki – saboda shi’ancinsa – ya yi ta nuna ma Tattar goyon baya da ba su asirran Musulmi.

A kodayaushe yana aika masu wasiku. Sai na biyu shi ne sarkin garin Musil wanda ake ma lakabi da Al-Malik Ar- Rahim. Wannan sarki shi ma ya dade yana sarauta (tsawon shekaru 50), kuma dan Shi’ah ne da ya raya wasu al’adu da bukukuwa na kiristoci, ya kuma kulla alaka mai karfi da Tattar har da aurar da dansa Salihu ga ‘yar sarkin Tattar na wancan lokaci Hulako, duk da yake auren bai yi karko ba kuma ya haifar da rashin jituwa a tsakanin su amma dai ya ba da goyon baya da gudunmawa ga Tattar har ma mayakansa sun taimaka wajen yakar Bagadaza. Na uku shi ne uwa uba ga wannan al’amari, ina nufin Waziri Mu’ayyiduddin Muhammad Ibnu Ahmad Ibnul Alkami wanda ya hau mukamin waziri a zamanin sarki Musta’asim tsawon shekaru 14. Kuma ya yi iya kokarinsa ya daukaka shi’anci amma Ahlus- Sunnah suka rinjaye shi, sai ya bi ta hanyar hila da makirci kamar yadda muka riga muka fada.

Tarihin
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
Gidan Da Aka Farmaka A Bauchi Ba Na Shugaban INEC Ba Ne – Oyekanmi

Gidan Da Aka Farmaka A Bauchi Ba Na Shugaban INEC Ba Ne - Oyekanmi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.