ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shinge 4 Da Sabon Gwamnan Zamfara Ya Tsallake Kafin Ya Doke Matawalle

by Bello Hamza
3 years ago
Zamfara

A ranar Talata 21 ga watan Maris 2023 ne al’ummar Nijeriya suka tashi da labarin wata girgiza fagen siyasar kasar nan, inda aka sanar da cewa, dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP Dakta Dauda Lawal Dare, ya lashe zaben da aka yi na gwamna a ranar 18 ga watan Maris 2023 a Jihar Zamfara, inda ya yi waje rod da gwamna mai ci na jam’iyyar APC, Daklta Bello Matawalle.

Jami’in kula da zaben da aka yi, Farfesa Kasimu Shehu, ya sanar da cewa, sakamakon zaben da aka yi ya nuna cewa, Dauda Dare ya samu kuri’a 377,726 inda ya kayar da Matawalle wanda ya tashi da kuri’a 311,976.

  • Maraba Da Azumin Ramadan Na Bana
  • Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun

Tuni aka barke da murnar wannan nasarar da Lawal na PDP ya samu a sassan jihar Zamfara dama Nijeriya baki daya, nasarar da ake gani lallai ta samu ne ta hanyar jajircewa da aiki tukuru daga Dan takarar Dakta Lawal da bangaren jam’iyyar PDP gaba daya.

ADVERTISEMENT

Tabbas wannan nasarar ta Dauda Lawal bata zo da sauki ba, ya ci karo da shingaye da dama. Dauda wanda tsohon ma’aikacin Banki ne ya fuskanci shari’u da dama har zuwa makonni kadan kafin a fuskanci zaben, shari’un neman tabbatar da shi a matsayin dan takarar gwamnan Zamfara, amma cikin ikon Allah ya samu nasara a dukkan shari’un da ya fuskanta.

Tun farko a watan Satumba na shekarar 20022, wata kotun tarayya da ke Gusau ta soke takararsa kan cewa, taron da aka yi inda aka zabe shi a mastayin dan takarar ba halastacciya ba ne, wani tsohon dan majalisar tarayya ne mai suna Alhaji Ibrahim Shehu Gusau, ya nemi kotu ta soke zaben, a cewarsa an tafka magudi a zabukkan da aka yi. Maishari’a Aminu Bappa ya soke zaben a ranar 25 ga wata Mayu 2022 inda ya nemi a sake gudanar da wani zaben fidda gwani.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Duk da cewa, Lawal ya sake lashe zaben fidda gwani da aka yi amma kotun ta kuma dakatar da aiwatar da zaben sa da aka yi.

Haka kuma Maishari’a Bappa ya sake soke zaben ya kuma zartar da cewa, jam’iyyar PDP ba za ta iya gabatar da dan takarar a jihar Zamfara a zaben 2023 gaba daya ba.

Amma Lawal bai sadakar ba, inda shi da Adamu Maina-Waziri, shugaban kwamitin da ya gudanar da zaben fidda gwamni Kanal Bala Mande (mai Ritaya) suka daukaka kara a babban kotun daukaka kara na Sakwatto inda suka nemi kotu da soke umarnin.

A watan Janairu na 2023 babbar kotun a karkashin Maishari’a Abubakar Talba, ta yi watsi da hukunci inda ta sake amincewa da Dakta Lawal a matsayin dan takarar jam’iyyar PDP a zaben da za a yi.

Karin shinge

Duk da wadannan nasarorin da Lawal ya samu, sai gashi an daukaka karar zuwa kotun koli. Inda a ranar 6 ga watan Maris 2023, ya sake samun nasarar a kotun koli inda ta zartar da cewa, Lawal ne halastaccen dan takarar jam’iyyar PDP kuma shi ne zai tsaya mata takara a zaben 2023.

Haka kuma Lawal ya fuskanci shari’a daga hukumar EFCC, inda shari’ar ta kai ga kotun koli amma cikin ikon Allah Lawal ya samu cikakken nasara inda kotun ta wanke shi daga dukkan zarge-zarge.

Daga ranar 29 ga watan Mayu na shekarar 2023 Dakta Lawal Dare zai karbi ragamar mulki Jihar Zamfara daga hannun Bello Matawale inda zai cigaba da aiwatar da alkawuran da ya yi wa la’umma, muna fatan al’umma za su bashi dukkan goyon bayan da yake bukata don kai Jihar Zamfa tudun-mun-tsira.

Zamfara
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Tarihin Mamayar Tattar 4

Tarihin Mamayar Tattar 4

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.