• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Dan Majalisar Tarayya, Ibrahim IMBA Ya Sauya Sheka Zuwa APC

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Siyasa
0
Tsohon Dan Majalisar Tarayya, Ibrahim IMBA Ya Sauya Sheka Zuwa APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon dan majalisar wakilai ta tarayya kuma dan takarar Sanatan Bauchi ta Arewa a karkashin jam’iyar Social Democratic Party (SDP) a zaben 2023, Hon. Ibrahim Mohammed Baba IMBA ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

IMBA wanda ya shelanta komawa jam’iyyar a ranar Juma’a kuma ya samu tarba daga wajen shugaban jam’iyyar APC a gundumar Nasarawa Bakin Kasuwa a karamar hukumar Katagum, Adamu Abubakar da suka karbe shi a ofishin jam’iyyar da ke gundumar.

  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 8, Ya Jikkata 7 A Bauchi
  • Gwamnan Bauchi Ya Nada Sarkin Ningi A Matsayin Amirul Hajj Na 2023

IMBA ya kasance dan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Katagum tsakanin shekarar 2015 zuwa 2019 da ya samu nasarar tafiya majalisar a karkashin jam’iyyar APC daga bisani kuma ya fice daga jam’iyyar bayan wasu ‘yan matsaloli.

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida kan dalilinsa na sake dawowa cikin jam’iyyar APC, Ibrahim Baba IMBA ya ce sun dawo tare da magoya bayansa ne domin gina jam’iyyar da sake farfado da ita, kana ya na mai cewa dukkanin matakan da suka dace na gyara jam’iyyar za su yi.

Ya ce, “Babban dalilina shi ne muna son mu dawo mu sake gina ita jam’iyyar saboda ta dawo hayyacinta. Kamar a 2015 an fusata mutane da yawa, mutane sun yi fushi sosai a jihar Bauchi saboda wasu dalilai, hakan ya sanya wadansunmu suka fita, wasu sun dawo wasu kuma har yanzu ba su dawo ba, wasu kuma har yanzu din su na cikin jam’iyyar amma ba su taimakonta.

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

“Wannan dalilin ya sanya muka ce bar mu dawo domin a zo a gyara tsarin.”

Ya ce su na sane har yanzu har gobe hankalin al’ummar jihar Bauchi na kan jam’iyyar APC, “Dawowarmu din zai taimaka wajen shawo kan matsalolin da ake fama da su musamman rikicin cikin gidan nan. Idan muka samu zo muka zauna muka samu wadanda lamarin ya shafa tun da mu din ma mun fita amma mun san ciwon da ya sa muka fita, don haka da yardar Allah za mu samu masu ruwa da tsaki a zo a ga an zauna da su domin tabbatar jam’iyyar ta sake samun nasara a gaba kuma al’umma su mori nasarar da aka samu.”

A cewarsa, babu abun da tattaunawa ba zai gyara shi ba, don haka ya ce rikicin cikin gida da ke APC za su yi kokarin magance shi nan ba da jimawa ba, “Duk lokacin da mutane suka zauna suka fitar da abubuwan da suke ganin ya dace a yi da wadanda suke ganin bai dace a yi ba, ta haka za a samu mafita kan matsaloli sosai.”

IMBA ya kuma shaida cewar sai da ya tuntubi magoya bayansa da masu ruwa da tsaki kafin daukan wannan matakin inda suka mara masa baya tare da sake biyo shi suka dawo APC.

“Na tuntubi magoya bayana sosai kafin muka dauki wannan matakin, kuma tun lokacin da muka koma ita wancan jam’iyyar har muka yi takara magoya bayana da dama basu fito sun shiga wancan jam’iyyar ba, sun dai je sun mara mana baya ne a zabe wanda kowa ya ga yadda zaben ya kasance musamman a karamar hukumata ta Katagum, wannan dalilin ya sanya dole mu sauraresu mu dawo mu kula da wadanda suka fi bukatar mu yi mu’alamar siyasa da su.”

Shi ma a nasa bangaren, shugaban jam’iyyar APC a gundumar Nasarawa Bakin Kasuwa a karamar hukumar Katagum, Adamu Abubakar, ya nuna jin dadinsu bisa dawowar IMBA cikin jam’iyyar, yana mai cewa tabbas jam’iyyar cike take da farin cikin samun irinsa lura da irin tasirin da ke da shi a siyasance.

Ya kuma bada tabbacin cewa a matsayinsa na mai fada a ji, zai kawo cigaba musamman wajen tabbatar da hadin kai da cigaban jam’iyyar, sai ya masa lale da dawowa jam’iyyarsa ta asali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiDan Majalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kashe Fitacciyar Mawaƙiyar Nan Ta Sudan Shaden Gardoodd

Next Post

Labarin Dutsen Nyiragongo Mai Dauke Da Tsawa

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

1 day ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

2 days ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

2 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

3 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

6 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 week ago
Next Post
Labarin Dutsen Nyiragongo Mai Dauke Da Tsawa

Labarin Dutsen Nyiragongo Mai Dauke Da Tsawa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.