ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Dan Majalisar Tarayya, Ibrahim IMBA Ya Sauya Sheka Zuwa APC

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Dan majalisa

Tsohon dan majalisar wakilai ta tarayya kuma dan takarar Sanatan Bauchi ta Arewa a karkashin jam’iyar Social Democratic Party (SDP) a zaben 2023, Hon. Ibrahim Mohammed Baba IMBA ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

IMBA wanda ya shelanta komawa jam’iyyar a ranar Juma’a kuma ya samu tarba daga wajen shugaban jam’iyyar APC a gundumar Nasarawa Bakin Kasuwa a karamar hukumar Katagum, Adamu Abubakar da suka karbe shi a ofishin jam’iyyar da ke gundumar.

  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 8, Ya Jikkata 7 A Bauchi
  • Gwamnan Bauchi Ya Nada Sarkin Ningi A Matsayin Amirul Hajj Na 2023

IMBA ya kasance dan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Katagum tsakanin shekarar 2015 zuwa 2019 da ya samu nasarar tafiya majalisar a karkashin jam’iyyar APC daga bisani kuma ya fice daga jam’iyyar bayan wasu ‘yan matsaloli.

ADVERTISEMENT

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida kan dalilinsa na sake dawowa cikin jam’iyyar APC, Ibrahim Baba IMBA ya ce sun dawo tare da magoya bayansa ne domin gina jam’iyyar da sake farfado da ita, kana ya na mai cewa dukkanin matakan da suka dace na gyara jam’iyyar za su yi.

Ya ce, “Babban dalilina shi ne muna son mu dawo mu sake gina ita jam’iyyar saboda ta dawo hayyacinta. Kamar a 2015 an fusata mutane da yawa, mutane sun yi fushi sosai a jihar Bauchi saboda wasu dalilai, hakan ya sanya wadansunmu suka fita, wasu sun dawo wasu kuma har yanzu ba su dawo ba, wasu kuma har yanzu din su na cikin jam’iyyar amma ba su taimakonta.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

“Wannan dalilin ya sanya muka ce bar mu dawo domin a zo a gyara tsarin.”

Ya ce su na sane har yanzu har gobe hankalin al’ummar jihar Bauchi na kan jam’iyyar APC, “Dawowarmu din zai taimaka wajen shawo kan matsalolin da ake fama da su musamman rikicin cikin gidan nan. Idan muka samu zo muka zauna muka samu wadanda lamarin ya shafa tun da mu din ma mun fita amma mun san ciwon da ya sa muka fita, don haka da yardar Allah za mu samu masu ruwa da tsaki a zo a ga an zauna da su domin tabbatar jam’iyyar ta sake samun nasara a gaba kuma al’umma su mori nasarar da aka samu.”

A cewarsa, babu abun da tattaunawa ba zai gyara shi ba, don haka ya ce rikicin cikin gida da ke APC za su yi kokarin magance shi nan ba da jimawa ba, “Duk lokacin da mutane suka zauna suka fitar da abubuwan da suke ganin ya dace a yi da wadanda suke ganin bai dace a yi ba, ta haka za a samu mafita kan matsaloli sosai.”

IMBA ya kuma shaida cewar sai da ya tuntubi magoya bayansa da masu ruwa da tsaki kafin daukan wannan matakin inda suka mara masa baya tare da sake biyo shi suka dawo APC.

“Na tuntubi magoya bayana sosai kafin muka dauki wannan matakin, kuma tun lokacin da muka koma ita wancan jam’iyyar har muka yi takara magoya bayana da dama basu fito sun shiga wancan jam’iyyar ba, sun dai je sun mara mana baya ne a zabe wanda kowa ya ga yadda zaben ya kasance musamman a karamar hukumata ta Katagum, wannan dalilin ya sanya dole mu sauraresu mu dawo mu kula da wadanda suka fi bukatar mu yi mu’alamar siyasa da su.”

Shi ma a nasa bangaren, shugaban jam’iyyar APC a gundumar Nasarawa Bakin Kasuwa a karamar hukumar Katagum, Adamu Abubakar, ya nuna jin dadinsu bisa dawowar IMBA cikin jam’iyyar, yana mai cewa tabbas jam’iyyar cike take da farin cikin samun irinsa lura da irin tasirin da ke da shi a siyasance.

Ya kuma bada tabbacin cewa a matsayinsa na mai fada a ji, zai kawo cigaba musamman wajen tabbatar da hadin kai da cigaban jam’iyyar, sai ya masa lale da dawowa jam’iyyarsa ta asali.

Dan majalisa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Labarin Dutsen Nyiragongo Mai Dauke Da Tsawa

Labarin Dutsen Nyiragongo Mai Dauke Da Tsawa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.