ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Dan Majalisar Tarayya, Ibrahim IMBA Ya Sauya Sheka Zuwa APC

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Dan majalisa

Tsohon dan majalisar wakilai ta tarayya kuma dan takarar Sanatan Bauchi ta Arewa a karkashin jam’iyar Social Democratic Party (SDP) a zaben 2023, Hon. Ibrahim Mohammed Baba IMBA ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

IMBA wanda ya shelanta komawa jam’iyyar a ranar Juma’a kuma ya samu tarba daga wajen shugaban jam’iyyar APC a gundumar Nasarawa Bakin Kasuwa a karamar hukumar Katagum, Adamu Abubakar da suka karbe shi a ofishin jam’iyyar da ke gundumar.

  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 8, Ya Jikkata 7 A Bauchi
  • Gwamnan Bauchi Ya Nada Sarkin Ningi A Matsayin Amirul Hajj Na 2023

IMBA ya kasance dan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Katagum tsakanin shekarar 2015 zuwa 2019 da ya samu nasarar tafiya majalisar a karkashin jam’iyyar APC daga bisani kuma ya fice daga jam’iyyar bayan wasu ‘yan matsaloli.

ADVERTISEMENT

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida kan dalilinsa na sake dawowa cikin jam’iyyar APC, Ibrahim Baba IMBA ya ce sun dawo tare da magoya bayansa ne domin gina jam’iyyar da sake farfado da ita, kana ya na mai cewa dukkanin matakan da suka dace na gyara jam’iyyar za su yi.

Ya ce, “Babban dalilina shi ne muna son mu dawo mu sake gina ita jam’iyyar saboda ta dawo hayyacinta. Kamar a 2015 an fusata mutane da yawa, mutane sun yi fushi sosai a jihar Bauchi saboda wasu dalilai, hakan ya sanya wadansunmu suka fita, wasu sun dawo wasu kuma har yanzu ba su dawo ba, wasu kuma har yanzu din su na cikin jam’iyyar amma ba su taimakonta.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Wannan dalilin ya sanya muka ce bar mu dawo domin a zo a gyara tsarin.”

Ya ce su na sane har yanzu har gobe hankalin al’ummar jihar Bauchi na kan jam’iyyar APC, “Dawowarmu din zai taimaka wajen shawo kan matsalolin da ake fama da su musamman rikicin cikin gidan nan. Idan muka samu zo muka zauna muka samu wadanda lamarin ya shafa tun da mu din ma mun fita amma mun san ciwon da ya sa muka fita, don haka da yardar Allah za mu samu masu ruwa da tsaki a zo a ga an zauna da su domin tabbatar jam’iyyar ta sake samun nasara a gaba kuma al’umma su mori nasarar da aka samu.”

A cewarsa, babu abun da tattaunawa ba zai gyara shi ba, don haka ya ce rikicin cikin gida da ke APC za su yi kokarin magance shi nan ba da jimawa ba, “Duk lokacin da mutane suka zauna suka fitar da abubuwan da suke ganin ya dace a yi da wadanda suke ganin bai dace a yi ba, ta haka za a samu mafita kan matsaloli sosai.”

IMBA ya kuma shaida cewar sai da ya tuntubi magoya bayansa da masu ruwa da tsaki kafin daukan wannan matakin inda suka mara masa baya tare da sake biyo shi suka dawo APC.

“Na tuntubi magoya bayana sosai kafin muka dauki wannan matakin, kuma tun lokacin da muka koma ita wancan jam’iyyar har muka yi takara magoya bayana da dama basu fito sun shiga wancan jam’iyyar ba, sun dai je sun mara mana baya ne a zabe wanda kowa ya ga yadda zaben ya kasance musamman a karamar hukumata ta Katagum, wannan dalilin ya sanya dole mu sauraresu mu dawo mu kula da wadanda suka fi bukatar mu yi mu’alamar siyasa da su.”

Shi ma a nasa bangaren, shugaban jam’iyyar APC a gundumar Nasarawa Bakin Kasuwa a karamar hukumar Katagum, Adamu Abubakar, ya nuna jin dadinsu bisa dawowar IMBA cikin jam’iyyar, yana mai cewa tabbas jam’iyyar cike take da farin cikin samun irinsa lura da irin tasirin da ke da shi a siyasance.

Ya kuma bada tabbacin cewa a matsayinsa na mai fada a ji, zai kawo cigaba musamman wajen tabbatar da hadin kai da cigaban jam’iyyar, sai ya masa lale da dawowa jam’iyyarsa ta asali.

Dan majalisa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Labarin Dutsen Nyiragongo Mai Dauke Da Tsawa

Labarin Dutsen Nyiragongo Mai Dauke Da Tsawa

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.