• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Cutar Hawan Jini Ke Kisan Mummuke A Nijreriya

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Rahotonni
0
Yadda Cutar Hawan Jini Ke Kisan Mummuke A Nijreriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cutar Hawan jini da aka fi sani da ‘Hypertension’ a turance ta zama matsalar lafiya da ke shafar miliyoyin al’umma a sasan duniya, wanda hakan ya sa zama wata barazana ga al’ummar kasa baki daya. Bawai a Nijeriya kawai cutar ke kisan bayar da tsoro ba lamari ne da ya shafi duniya baki daya.

Duniya ta san yadda cutar ke hallaka jama’a a kan haka ta ware rana ta musamman don a yi amfani da ita wajen fadakar da al’umma a ko ina a duniya yadda cutar take shiga kamar barawo tana hallaka mutane.

  • Buhari Ya Karrama Marigayi Sam Nda-isaiah Da Lambar Yabo Ta OFR

A duk ranar 17 ga watan Mayu, al’umma kan hadu don tunatar da juna tare da ankarar da mutane a kan bukata da muhimmanci gwajin hawan jini don sanin matsayin cutar a gare mu ta yadda za mu ci gaba da rayuwa da cutar ta tsawon lokaci.

Sau da yawa ana yi wa cutar hawan jini lakabi da “Mai kisan mummuke’ saboda yadda cutar ba ta nuna wasu manyan alamomi lokacin har sai ta kai ga mataki na kisa, wanda shigar da take yi a shiru shi kuma ke kai ga barazanar kamuwa da cuttutuka masu kisa kamar cutar zuciya, shanyewar bangaren jiki data koda da wasu cuttutuka da suka shafi zuciya.

Rahoton Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta bayyana cewa, cutar hawan jini na kashe mutum fiye da miliyan 9 a fadin duniya. A Nijeriya kuma yadda cutar ke hallaka al’umma nada ban tsoro don ita ke da alhakin mutuwar akalla mutum daya a cikin duk mutuwa uku da aka yi a kasar, don zaka samu yana fama da cutar.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Gidauniyar kula da cututtukan zuciya ta kasa ta sanar da cewa, cutar hawan jini ta kai a kalla kashi 38.1 na cuttukar da ke addabar al’umma. Inda aka ce kashi 38.1 na akalla al’ummar Nijeriya da sun kai miliyan 200 ya nuna cewa, kenan kusan mutum miliyan 26.7 na ‘yan Nijeriya na fama da cutar hawan jini kenan, lalle wannan abin takaici ne.

Haka kuma kungiyar likitoci ta kasa ta bayyana cewa, ‘yan Nijeriya na kashe Naira Miliyan 15.9 in aka kiyasata kudin magani a N15,964.76 a duk wata. Wannan ba karamin rikici ba ne a kasar da mutum miliyan 133 ke rayuwa a cikin talauci, kudin karbar maganin cutar hawan jini ya fi karfin kusan kashi 50 na al’umma Nijeriya. Masana harkokin kiwon lafiya sun tayyana cewa, abubuwan da suka shafi matsalar tsaro dana tattalin arzki sun kara karuwar cutar hawan jini a tsakanin ‘yan Nijeriya.

A wani sabon bincike da aka yi kwanan nan, an nuna cewa amfani da wayar salula yana taimakawa wajen hauhawar cutar ta hawan jini.

A ra’ayin wannan jaridar, sakamakon cutar hawan jini da ba a sha mata magani yana da tsananin gaske, nauyin tana hawa ne a kan wanda ke fama da cutar da ‘yanuwansu da kuma hukumomin kula da kiwon lafiya.

An kiyasta cewa, cutar hawan jini ce keda kashi 24 na kusan kashi 45 na matsalolin cututtutar da suka shafi cutar zuciya da ake samu a fadin tarayyar kasar nan, ba tare da wata shakka ba tabbas wannan ya zama lamari me tayar da hankali.

Taken bikin ranar cutar hawan jini ta wannan shekarar “Gwada hawan jininka, ka lura da shi don tsawaita rayuwa da shi ya yi daidai, ‘’wannan na kara nuna muhimmacin gwajin hawan jini a matsayin mataki na farko na maganin cutar.

Gyara hanyar rayuwa na daya daga cikin matakan da suka dace a yi amfani da su wajen rage barnar da cutar ke yi, cin abinci mai inganci da ke tattare da ganyayyaki, kayan lambu da sauransu da kuma rage amfani da gishiri a cikin abinci da rage amfani da abinci mai yawan suga.

Motsa jiki a kai-akai ta hanayr tafiya a kasa, hawa keke yana taimakawa wajen daidaita jinin da ke jikin mutum, ya kuma kamata a guje wa shan taba da barasa, don yin haka yana taimakwa wajen dakile hauhawar cutar.
Ga wasu mutane, motsa jiki kadai ba zai taimaka ba, ya kamata su lizimci amfani da magunguna su kamar yadda likita ya basu tare da kuma gwajin hawan jinin, ta haka ne likitan zai iya neman a rage ko a kara yawan maganin da ake sha tare da rage matsalolin da suka iya faruwa sakamakoin shan magunguna hawan jinin.

Maganin cutar hawan jini na bukatar hadin gwiwar kowa da kowa ciki har da gwamnati, jami’an lafiya da masu fama da cutar.

A ra’ayinmu ya kamata ta karfafa wayar wa da al’umma kai su kuma tabbatar da rage kudaden magunguna hawan jinin ta yadda al’umma za su samu saukin sayen magungunan da kuma samar da na’u’rorin gwajin cutar a cikin sauki.

Yana kuma da matukar muhimmanci, a wanna rana ta Hawan Jini na duniya kowa da kowa ciki har da yara kanana, tsofaffi su fahimmci illar da kisan mummuken da cutar hawan jini yake yi ga a cikin al’umma su kuma hada hannu wajen daukar matakin dakile shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwa 10 Da Zaku So Sani Cikin Jawabin Bankwana Da Buhari Ya Yi Wa ‘Yan Nijeriya

Next Post

Dogaro Da Man Fetur Ne Ya Jefa Nijeriya Matsin Tattalin Arziki -Oramah

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

2 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

2 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

3 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

3 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

4 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

4 weeks ago
Next Post
Dogaro Da Man Fetur Ne Ya Jefa Nijeriya Matsin Tattalin Arziki -Oramah

Dogaro Da Man Fetur Ne Ya Jefa Nijeriya Matsin Tattalin Arziki -Oramah

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

August 10, 2025
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.