ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Cutar Hawan Jini Ke Kisan Mummuke A Nijreriya

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Hawan jini

Cutar Hawan jini da aka fi sani da ‘Hypertension’ a turance ta zama matsalar lafiya da ke shafar miliyoyin al’umma a sasan duniya, wanda hakan ya sa zama wata barazana ga al’ummar kasa baki daya. Bawai a Nijeriya kawai cutar ke kisan bayar da tsoro ba lamari ne da ya shafi duniya baki daya.

Duniya ta san yadda cutar ke hallaka jama’a a kan haka ta ware rana ta musamman don a yi amfani da ita wajen fadakar da al’umma a ko ina a duniya yadda cutar take shiga kamar barawo tana hallaka mutane.

  • Buhari Ya Karrama Marigayi Sam Nda-isaiah Da Lambar Yabo Ta OFR

A duk ranar 17 ga watan Mayu, al’umma kan hadu don tunatar da juna tare da ankarar da mutane a kan bukata da muhimmanci gwajin hawan jini don sanin matsayin cutar a gare mu ta yadda za mu ci gaba da rayuwa da cutar ta tsawon lokaci.

ADVERTISEMENT

Sau da yawa ana yi wa cutar hawan jini lakabi da “Mai kisan mummuke’ saboda yadda cutar ba ta nuna wasu manyan alamomi lokacin har sai ta kai ga mataki na kisa, wanda shigar da take yi a shiru shi kuma ke kai ga barazanar kamuwa da cuttutuka masu kisa kamar cutar zuciya, shanyewar bangaren jiki data koda da wasu cuttutuka da suka shafi zuciya.

Rahoton Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta bayyana cewa, cutar hawan jini na kashe mutum fiye da miliyan 9 a fadin duniya. A Nijeriya kuma yadda cutar ke hallaka al’umma nada ban tsoro don ita ke da alhakin mutuwar akalla mutum daya a cikin duk mutuwa uku da aka yi a kasar, don zaka samu yana fama da cutar.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

Gidauniyar kula da cututtukan zuciya ta kasa ta sanar da cewa, cutar hawan jini ta kai a kalla kashi 38.1 na cuttukar da ke addabar al’umma. Inda aka ce kashi 38.1 na akalla al’ummar Nijeriya da sun kai miliyan 200 ya nuna cewa, kenan kusan mutum miliyan 26.7 na ‘yan Nijeriya na fama da cutar hawan jini kenan, lalle wannan abin takaici ne.

Haka kuma kungiyar likitoci ta kasa ta bayyana cewa, ‘yan Nijeriya na kashe Naira Miliyan 15.9 in aka kiyasata kudin magani a N15,964.76 a duk wata. Wannan ba karamin rikici ba ne a kasar da mutum miliyan 133 ke rayuwa a cikin talauci, kudin karbar maganin cutar hawan jini ya fi karfin kusan kashi 50 na al’umma Nijeriya. Masana harkokin kiwon lafiya sun tayyana cewa, abubuwan da suka shafi matsalar tsaro dana tattalin arzki sun kara karuwar cutar hawan jini a tsakanin ‘yan Nijeriya.

A wani sabon bincike da aka yi kwanan nan, an nuna cewa amfani da wayar salula yana taimakawa wajen hauhawar cutar ta hawan jini.

A ra’ayin wannan jaridar, sakamakon cutar hawan jini da ba a sha mata magani yana da tsananin gaske, nauyin tana hawa ne a kan wanda ke fama da cutar da ‘yanuwansu da kuma hukumomin kula da kiwon lafiya.

An kiyasta cewa, cutar hawan jini ce keda kashi 24 na kusan kashi 45 na matsalolin cututtutar da suka shafi cutar zuciya da ake samu a fadin tarayyar kasar nan, ba tare da wata shakka ba tabbas wannan ya zama lamari me tayar da hankali.

Taken bikin ranar cutar hawan jini ta wannan shekarar “Gwada hawan jininka, ka lura da shi don tsawaita rayuwa da shi ya yi daidai, ‘’wannan na kara nuna muhimmacin gwajin hawan jini a matsayin mataki na farko na maganin cutar.

Gyara hanyar rayuwa na daya daga cikin matakan da suka dace a yi amfani da su wajen rage barnar da cutar ke yi, cin abinci mai inganci da ke tattare da ganyayyaki, kayan lambu da sauransu da kuma rage amfani da gishiri a cikin abinci da rage amfani da abinci mai yawan suga.

Motsa jiki a kai-akai ta hanayr tafiya a kasa, hawa keke yana taimakawa wajen daidaita jinin da ke jikin mutum, ya kuma kamata a guje wa shan taba da barasa, don yin haka yana taimakwa wajen dakile hauhawar cutar.
Ga wasu mutane, motsa jiki kadai ba zai taimaka ba, ya kamata su lizimci amfani da magunguna su kamar yadda likita ya basu tare da kuma gwajin hawan jinin, ta haka ne likitan zai iya neman a rage ko a kara yawan maganin da ake sha tare da rage matsalolin da suka iya faruwa sakamakoin shan magunguna hawan jinin.

Maganin cutar hawan jini na bukatar hadin gwiwar kowa da kowa ciki har da gwamnati, jami’an lafiya da masu fama da cutar.

A ra’ayinmu ya kamata ta karfafa wayar wa da al’umma kai su kuma tabbatar da rage kudaden magunguna hawan jinin ta yadda al’umma za su samu saukin sayen magungunan da kuma samar da na’u’rorin gwajin cutar a cikin sauki.

Yana kuma da matukar muhimmanci, a wanna rana ta Hawan Jini na duniya kowa da kowa ciki har da yara kanana, tsofaffi su fahimmci illar da kisan mummuken da cutar hawan jini yake yi ga a cikin al’umma su kuma hada hannu wajen daukar matakin dakile shi.

Hawan jini
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Jihohi Suka Fara Ɗanɗana Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    ‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Noma
Rahotonni

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Next Post
Dogaro Da Man Fetur Ne Ya Jefa Nijeriya Matsin Tattalin Arziki -Oramah

Dogaro Da Man Fetur Ne Ya Jefa Nijeriya Matsin Tattalin Arziki -Oramah

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.