ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Cutar Hawan Jini Ke Kisan Mummuke A Nijreriya

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Hawan jini

Cutar Hawan jini da aka fi sani da ‘Hypertension’ a turance ta zama matsalar lafiya da ke shafar miliyoyin al’umma a sasan duniya, wanda hakan ya sa zama wata barazana ga al’ummar kasa baki daya. Bawai a Nijeriya kawai cutar ke kisan bayar da tsoro ba lamari ne da ya shafi duniya baki daya.

Duniya ta san yadda cutar ke hallaka jama’a a kan haka ta ware rana ta musamman don a yi amfani da ita wajen fadakar da al’umma a ko ina a duniya yadda cutar take shiga kamar barawo tana hallaka mutane.

  • Buhari Ya Karrama Marigayi Sam Nda-isaiah Da Lambar Yabo Ta OFR

A duk ranar 17 ga watan Mayu, al’umma kan hadu don tunatar da juna tare da ankarar da mutane a kan bukata da muhimmanci gwajin hawan jini don sanin matsayin cutar a gare mu ta yadda za mu ci gaba da rayuwa da cutar ta tsawon lokaci.

ADVERTISEMENT

Sau da yawa ana yi wa cutar hawan jini lakabi da “Mai kisan mummuke’ saboda yadda cutar ba ta nuna wasu manyan alamomi lokacin har sai ta kai ga mataki na kisa, wanda shigar da take yi a shiru shi kuma ke kai ga barazanar kamuwa da cuttutuka masu kisa kamar cutar zuciya, shanyewar bangaren jiki data koda da wasu cuttutuka da suka shafi zuciya.

Rahoton Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta bayyana cewa, cutar hawan jini na kashe mutum fiye da miliyan 9 a fadin duniya. A Nijeriya kuma yadda cutar ke hallaka al’umma nada ban tsoro don ita ke da alhakin mutuwar akalla mutum daya a cikin duk mutuwa uku da aka yi a kasar, don zaka samu yana fama da cutar.

LABARAI MASU NASABA

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Gidauniyar kula da cututtukan zuciya ta kasa ta sanar da cewa, cutar hawan jini ta kai a kalla kashi 38.1 na cuttukar da ke addabar al’umma. Inda aka ce kashi 38.1 na akalla al’ummar Nijeriya da sun kai miliyan 200 ya nuna cewa, kenan kusan mutum miliyan 26.7 na ‘yan Nijeriya na fama da cutar hawan jini kenan, lalle wannan abin takaici ne.

Haka kuma kungiyar likitoci ta kasa ta bayyana cewa, ‘yan Nijeriya na kashe Naira Miliyan 15.9 in aka kiyasata kudin magani a N15,964.76 a duk wata. Wannan ba karamin rikici ba ne a kasar da mutum miliyan 133 ke rayuwa a cikin talauci, kudin karbar maganin cutar hawan jini ya fi karfin kusan kashi 50 na al’umma Nijeriya. Masana harkokin kiwon lafiya sun tayyana cewa, abubuwan da suka shafi matsalar tsaro dana tattalin arzki sun kara karuwar cutar hawan jini a tsakanin ‘yan Nijeriya.

A wani sabon bincike da aka yi kwanan nan, an nuna cewa amfani da wayar salula yana taimakawa wajen hauhawar cutar ta hawan jini.

A ra’ayin wannan jaridar, sakamakon cutar hawan jini da ba a sha mata magani yana da tsananin gaske, nauyin tana hawa ne a kan wanda ke fama da cutar da ‘yanuwansu da kuma hukumomin kula da kiwon lafiya.

An kiyasta cewa, cutar hawan jini ce keda kashi 24 na kusan kashi 45 na matsalolin cututtutar da suka shafi cutar zuciya da ake samu a fadin tarayyar kasar nan, ba tare da wata shakka ba tabbas wannan ya zama lamari me tayar da hankali.

Taken bikin ranar cutar hawan jini ta wannan shekarar “Gwada hawan jininka, ka lura da shi don tsawaita rayuwa da shi ya yi daidai, ‘’wannan na kara nuna muhimmacin gwajin hawan jini a matsayin mataki na farko na maganin cutar.

Gyara hanyar rayuwa na daya daga cikin matakan da suka dace a yi amfani da su wajen rage barnar da cutar ke yi, cin abinci mai inganci da ke tattare da ganyayyaki, kayan lambu da sauransu da kuma rage amfani da gishiri a cikin abinci da rage amfani da abinci mai yawan suga.

Motsa jiki a kai-akai ta hanayr tafiya a kasa, hawa keke yana taimakawa wajen daidaita jinin da ke jikin mutum, ya kuma kamata a guje wa shan taba da barasa, don yin haka yana taimakwa wajen dakile hauhawar cutar.
Ga wasu mutane, motsa jiki kadai ba zai taimaka ba, ya kamata su lizimci amfani da magunguna su kamar yadda likita ya basu tare da kuma gwajin hawan jinin, ta haka ne likitan zai iya neman a rage ko a kara yawan maganin da ake sha tare da rage matsalolin da suka iya faruwa sakamakoin shan magunguna hawan jinin.

Maganin cutar hawan jini na bukatar hadin gwiwar kowa da kowa ciki har da gwamnati, jami’an lafiya da masu fama da cutar.

A ra’ayinmu ya kamata ta karfafa wayar wa da al’umma kai su kuma tabbatar da rage kudaden magunguna hawan jinin ta yadda al’umma za su samu saukin sayen magungunan da kuma samar da na’u’rorin gwajin cutar a cikin sauki.

Yana kuma da matukar muhimmanci, a wanna rana ta Hawan Jini na duniya kowa da kowa ciki har da yara kanana, tsofaffi su fahimmci illar da kisan mummuken da cutar hawan jini yake yi ga a cikin al’umma su kuma hada hannu wajen daukar matakin dakile shi.

Hawan jini
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

MASU ALAKA

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri
Rahotonni

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Next Post
Dogaro Da Man Fetur Ne Ya Jefa Nijeriya Matsin Tattalin Arziki -Oramah

Dogaro Da Man Fetur Ne Ya Jefa Nijeriya Matsin Tattalin Arziki -Oramah

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.