ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martanin Obaseki Ga Wike Kan Kiran Dakatar Da Atiku Daga PDP…

…Zai Ci Amanar APC Ba Da Jimawa Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Wike

Mamba a kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, Dakta Don Pedro Obaseki ya bayyana cewa ministan Abuja kuma tsohon gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ya ketare iyaka na kiran a dakatar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar.

Idan za a iya tunawa a wata tattaunawa da aka yi da Wike a gidan talabijin na Channels a shirin siyasa a yau, ya bayyana cewa, “Duba da wuraren da PDP ta yi rashin nasara saboda girman kai da kwadayi da kuma rashin adalci. Idan da PDP ta yi abin da ya kamata ta yi, to da ba wannan maganan ake ba a yanzu.

  • Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Nada Cardoso A Matsayin Sabon Gwamnan CBN

“Ya kamata a ce an yi adalci, wanda hakan ya sa nake kira da kwamitin gudanar-wa na jam’iyyar ya dakatar da dan takarar shugaban kasa da sauran wasu mutane kamar irin su Aminu Tambuwal domin sake gina jam’iyyar PDP.”

ADVERTISEMENT

Sai dai da yake mayar da martani a gaban ‘yan jarida a Abuja, Obaseki ya ce jiga-jigan jam’iyya mai mulki ta APC su shirya amsar cin amana daga wurin Wike, inda ya ce PDP ba za ta iya ci gaba da lamuntar duk wani cin kashi daga hannun Wike ba.

Ya ce, “Shi ne mafic in amanan jam’iyyar a tarihin siyasarmu. Ya raba gari da Ro-timi Amaechi da Goodluck Jonathan da Peter Odili da Atiku Abubakar, inda a yan-zu yake tare da Bola Tinubu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

“Wike ya fito fili ya bukaci a dakatar da shugaban jam’iyyarmu na kasa kuma dan takarar shugaban kasa na tutar jam’iyyar, wanda ‘yan Nijeriya suka amshe shi hannu bibiyu kamar yadda INEC ta gabatar da cewa mun lashe jihohi 21, sannan har ya nemi a dakatar da Atiku daga jam’iyyar, lallai Wike ya ketare iya a halin yanzu, ya kamata ya shirya yaki.

“Yana da kudin da zai iya yaki da mu, saboda muna zuwa gare shi kamar runduna. Na tabbata Wike ya karaci fannin shari’a. Na tabbata shi lauya ne kuma ya san cewa duk mai shirin zaman lafiya dole ya shirya wa yaki.

“Nyesom Wike ya tabo tsuliyar dodo, ya jira ya ga abin da zai same shi. Shawarar kawai da zan bayar ita ce, wadanda suka hada baki da shi suka ci amana wajen yi wa APC aiki, su jira karshensu.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

December 19, 2025
‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

December 19, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Tambarin Dimokuradiyya

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

November 28, 2025
Next Post
Neymar Ya Fara Wasansa Na Farko A Al Hilal Da Kafar Dama

Neymar Ya Fara Wasansa Na Farko A Al Hilal Da Kafar Dama

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.