• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Martanin Obaseki Ga Wike Kan Kiran Dakatar Da Atiku Daga PDP…

…Zai Ci Amanar APC Ba Da Jimawa Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Wike

Mamba a kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, Dakta Don Pedro Obaseki ya bayyana cewa ministan Abuja kuma tsohon gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ya ketare iyaka na kiran a dakatar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar.

Idan za a iya tunawa a wata tattaunawa da aka yi da Wike a gidan talabijin na Channels a shirin siyasa a yau, ya bayyana cewa, “Duba da wuraren da PDP ta yi rashin nasara saboda girman kai da kwadayi da kuma rashin adalci. Idan da PDP ta yi abin da ya kamata ta yi, to da ba wannan maganan ake ba a yanzu.

  • Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Nada Cardoso A Matsayin Sabon Gwamnan CBN

“Ya kamata a ce an yi adalci, wanda hakan ya sa nake kira da kwamitin gudanar-wa na jam’iyyar ya dakatar da dan takarar shugaban kasa da sauran wasu mutane kamar irin su Aminu Tambuwal domin sake gina jam’iyyar PDP.”

Sai dai da yake mayar da martani a gaban ‘yan jarida a Abuja, Obaseki ya ce jiga-jigan jam’iyya mai mulki ta APC su shirya amsar cin amana daga wurin Wike, inda ya ce PDP ba za ta iya ci gaba da lamuntar duk wani cin kashi daga hannun Wike ba.

Ya ce, “Shi ne mafic in amanan jam’iyyar a tarihin siyasarmu. Ya raba gari da Ro-timi Amaechi da Goodluck Jonathan da Peter Odili da Atiku Abubakar, inda a yan-zu yake tare da Bola Tinubu.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

“Wike ya fito fili ya bukaci a dakatar da shugaban jam’iyyarmu na kasa kuma dan takarar shugaban kasa na tutar jam’iyyar, wanda ‘yan Nijeriya suka amshe shi hannu bibiyu kamar yadda INEC ta gabatar da cewa mun lashe jihohi 21, sannan har ya nemi a dakatar da Atiku daga jam’iyyar, lallai Wike ya ketare iya a halin yanzu, ya kamata ya shirya yaki.

“Yana da kudin da zai iya yaki da mu, saboda muna zuwa gare shi kamar runduna. Na tabbata Wike ya karaci fannin shari’a. Na tabbata shi lauya ne kuma ya san cewa duk mai shirin zaman lafiya dole ya shirya wa yaki.

“Nyesom Wike ya tabo tsuliyar dodo, ya jira ya ga abin da zai same shi. Shawarar kawai da zan bayar ita ce, wadanda suka hada baki da shi suka ci amana wajen yi wa APC aiki, su jira karshensu.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Neymar Ya Fara Wasansa Na Farko A Al Hilal Da Kafar Dama

Neymar Ya Fara Wasansa Na Farko A Al Hilal Da Kafar Dama

LABARAI MASU NASABA

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.