ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kano: Ba Mu Yarda A Karya ‘Yancin Dimokuradiyya Ba – Kungiya

by Sulaiman
2 years ago
Kano

Gamayyar Ƙungiyoyin Kare ‘Yancin Dimokuraɗiyya (CDR) a Jihar Bauchi, sun nuna rashin amincewa da kuma yin tsokaci kan yadda Kotun Shari’ar Zaɓen Gwamnan Kano ta yanke hukuncin da ya haifar da shakku da zargin yunƙurin danne haƙƙin zaɓen da ɗimbin jama’a su ka yi, bisa kyakkyawan tsarin dimokuraɗiyya.

CDR ta hasala ne dangane da hukuncin da kotun a Kano ta yanke, cewa, jam’iyyar mai mulki a ƙasa, APC ce da ɗan takarar a zaɓen gwamna a Kano su ka yi nasara, ba Gwamna Abba Kabir Yusuf na NNPP ba, wanda INEC ta tabbatar.

  • Kotun Zaben Gwamnan Taraba: Cikin Matsi INEC Ta Ayyana Sakamako, A Sake Bitar Zaben – NNPP
  • Mun Dauki Darasi A Zaben 2023 – Shugaban INEC

“Akwai matuƙar buƙatar mu tunatar wa majiɓinta wannan al’amari da dukkan masu ruwa da tsaki cewa, Kano ita ce cibiya kuma ginshiƙin tattalin arzikin Nijeriya. “Don haka ƙoƙarin bijirowa ko cimma hargitsi na siyasa yanzu a Kano, abu ne da ka iya dagula wa ko tarwatsa jihohin Arewa.”

ADVERTISEMENT

 

“A matsayin mu na gamayyar ƙungiyoyin yaɗa dimokuraɗiyya da kishinta da kuma kare martabarta, mun ga ya kamata mu fito don a ji muryoyinmu don ganin cewa ba mu sa-ido an yi wa al’umma ƙwacen abin da su ka zaɓa ba, lamarin da ka iya haifar wa Kano da Arewa baki ɗaya mummunan sakamakon za a yi da-na-sanin afkuwar sa daga baya.

LABARAI MASU NASABA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

 

“Mu na ƙara nuni da cewa, mu fa ba mambobin NNPP ba ne, kuma ba ‘yan asalin Jihar Kano ba ne, amma dai akwai haƙƙi a kan mu da wajibcin fitowa mu yi gargaɗi ga dukkan masu hannu kan shirin wannan lamari”

A lokacin da ya ke jawabi yayin wani jerin-gwanon lumana ɗauke da kwalaye a ‘Tafawa Ɓalewa Tomb’, Daraktan Tsare-tsaren CDR mai suna Ibrahim Babayo, ya ce, “Kyakkyawan tsarin dimokraɗiyya shi ne ginshiƙin ɗorewar ƙasa. Kuma abu muhimmi shi ne a kare darajar kowace ƙuri’ar da jama’a suka kaɗa bisa adalci.”

 

Ya ce babban adalci ga kotun zaɓe shi ne ta yi ƙwaƙƙwaran binciken duk wani zargin aikata ba daidai ba a lokacin zaɓe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

October 5, 2024
Next Post
Xi Ya Jaddada Bukatar Bunkasa Tattalin Arzikin Kogin Yangtze Mai Inganci

Xi Ya Jaddada Bukatar Bunkasa Tattalin Arzikin Kogin Yangtze Mai Inganci

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025
Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.