• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Gwamnan Jihar California Dake Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
Xi Jinping

Da yammacin yau Laraba 25 ga wata ne, shuguban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da gwamnan jihar California ta kasar Amurka, Gavin Newsom, a babban dakin taron al’umma dake birnin Beijing.

Xi ya ce, cimma nasarori wajen raya dangantakar Sin da Amurka tun lokacin da har zuwa yanzu, ba abu mai sauki ba ne, wanda ya cancanci a daraja. Manufofin gwamnatin kasar Sin kan Amurka, har kullum su ne, mutunta juna, da zaman jituwa, da yin hadin-gwiwa bisa cimma moriyar juna. Kasar Sin za ta ci gaba da yin kokari a wannan fanni, kana, tana fatan Amurka za ta bada hadin-kai.

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Fashin Daji Da Dama, Sun Kwato Makamai A Sokoto
  • Gasar Wasannin Asiya Ajin Masu Bukata Ta Musaman Ta Hangzhou Ta Bayyana Kulawar Da Sin Take Baiwa Wannan Rukuni Na Al’umma

A nasa bangaren, Gavin Newsom ya ce, babu wata dangantakar kasa da kasa a duniya da ta fi dangantakar Amurka da Sin muhimmanci, dangantakar da ta shafi makomar Amurka gami da alfanun al’ummar kasar. Ya yarda da manufofin da shugaba Xi ya bayyana wajen raya dangantakar kasashen biyu, da shaida aniyar kara tuntubar juna tsakanin jiharsa wato California da kasar Sin, da fadada hadin-gwiwarsu a fannonin da suka shafi sauyin yanayi da sabbin makamashi. California din tana son zama kakkarfar abokiyar hadin-gwiwar kasar Sin na dogon lokaci. Bugu da kari, a yau ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika wasikar taya murnar bikin ba da lambar yabo na kwamitin kula da dangantakar da ke tsakanin kasashen Amurka da Sin na kasar Amurka.

Shugaba Xi Jinping ya yabawa kwamitin bisa kokarin sa kaimi ga inganta mu’amala da hadin gwiwa a tsakanin Amurka da Sin a fannoni daban daban, kana ya taya Henry Alfred Kissinger, murnar samun lambar yabon.

Shugaba Xi ya yi nuni da cewa, a matsayin manyan kasashe biyu a duniya, yadda Sin da Amurka suke mu’amala da juna ta hanya mai dacewa ko a’a, yana da nasaba da makomar zaman lafiya da bunkasuwa da kuma dan Adam a duniya. Ya ce Sin tana son bin ka’idojin girmama juna, da yin zaman tare cikin lumana, da yin hadin gwiwa don samun moriyar juna, da kara hadin gwiwa tare da kasar Amurka, da daidaita sabanin da ke tsakaninsu, da tinkarar kalubalen duniya tare, don samun moriyar juna, da wadata tare, da kuma amfanawa jama’ar kasashen biyu har ma da duk duniya baki daya.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Shugaba Xi yana fatan kwamitin da kuma abokai daga bangarori daban daban za su ci gaba da nuna goyon baya ga raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka don taka muhimmiyar rawa wajen sa kaimi ga raya dangantakar kasashen biyu yadda ya kamata.
Kana a wannan rana, shugaban kasar Amurka Joseph Biden shi ma ya mika wasikar taya murnar bikin. (Murtala Zhang, Zainab)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Next Post
Pedri Ba Zai Buga El-Clasico Ba Saboda Rauni

Pedri Ba Zai Buga El-Clasico Ba Saboda Rauni

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.