• English
  • Business News
Thursday, August 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akidar Siyasar Malam Aminu Kano Da Ta ‘Yan Siyasar Yanzu A Mizani –Farfesa Habu

Mun wallafa a 27 ga Janairu, 2023

by Leadership Hausa
2 years ago
in Rahotonni
0
Akidar Siyasar Malam Aminu Kano Da Ta ‘Yan Siyasar Yanzu A Mizani –Farfesa Habu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

FARFESA HABU MUHAMMAD, fitacce ne a Jami’ar Bayero da ma sauran jami’oin gida da na waje, mutun ne mai kishin ganin an inganta tsarin Dimokuradiyya, da kyakkyawan shugabanci a Nijeriya baya ga zamowar sa cikin masu kyakyawar fahimta a kan al’adu da harshen Hausa. Watanni biyu da suka gabata, ya zama shugaban cibiyyar nazarin kimiyyar siyasa da ke gidan tunawa da marigayi Malam Aminu Kano, wanda aka fi sani da Gidan Mumbayya da ke karkashin Jami’ar Bayero ta Kano. Wakilinmu MUSTAPA IBRAHIM KANO ya tattauna da shi kan akidar siyasar Malam Aminu Kano, daya daga cikin mazan jiya ‘yan gwagwarmaya, da kuma ta ‘yan siyasar wannan zamanin. Har ila yau da sauran wasu al’amura da aka bullo da su a cibiyar wanda za a rika gabatarwa da harshen Hausa zalla, ga dai tattaunawar kamar haka:

Da farko za mu so ka gabatar da kanka…

Sunana Farfesa Habu Muhammad, ni ne Babban Darakta ko kuma in ce, Shugaban Cibiyar Nazarin Kimiyyar Siyasa, da ke Gidan tunawa da Malam Aminu Kano, wato Gidan Mumbayya, da ke karkashin Jami’ar Bayero ta Kano. Na zama Daraktan wannan cibiya ne a ranar 6 ga Oktoban 2022. Hakan ta kasance ne bayan mutumin da na gada Farfesa Zango ya kammala wa’adin aikinsa na jagorancin gidan da ke Unguwar Gwammaja, a Karamar Hukumar Dala.

Farfesa bari mu dan yi waiwaye adon tafiya, ko za ka dora akidar siyasar Malam Aminu Kano da ta ‘yan siyasar yau a mizani?

To ita siyasa irin ta su Malam Aminu Kano siyasa ce ta a kida ta a `yantar da talaka daga kangin bauta da wulakanci da ake wa talaka a wancan lokacin, kuma siyasa ce ta neman `yanci domin sun san, ko mene ne ‘yanci domin ko ba komai sun yi gwagwarmaya da gumurzu na shan wahala da suka samu daga turawan mulkin mallaka kan maganar `yanci. To ka ga wasu daga cinkin su ko su Malam Aminu Kano suna da wannann ilimin kuma suna da wannan ruhin na neman `yanci cikin wahala da azaba da matsaloli daban-daban.

Labarai Masu Nasaba

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Saboda haka za ka ga siyasar su Malam Aminu Kano siyasa ce ta neman `yancin talaka, da `yantar da shi daga kangin bauta da za ka iya cewa masu gudanar da mulki na wancan lokacin sun sa talaka a kangin bauta, haka ne ma ya sa su Malam Aminu Kano da sauran `yan siyasar zamaninsa suke da wani take na SAWABA-SAWABA, to abin da suke nufi a wancan lokacin nasu shi ne irin abin da suke wa talaka na karbar haraji, da jangali, da sa mutum noma a gonar Rogo, ko makamancin haka ba tare da an biya shi ba, to wannan da wasu abu masu kama da wannan shi ne abin da su Malam Aminu Kano suka yi yaki da shi a tafiyarsu ta NEPU da PRP kuma wannan za ka ga cewa ita ce a kidar su Malam Aminu Kano da sauransu.

Kuma har ila yau wani abin lura, su, su Malam Aminu Kano babu batun tara kudi a akidar su illa dai kawai `yancin talaka, da biya masa bukata daidai gwargwadon iko, ka ga babu maganar cin hanci da rashawa da almundahana amma na yanzu mafiyawa daga cikinsu ko 99 bisa 100 suna kokarin tara abin duniya ne har ma ya fi karfin bukatarsu ta rayuwa. To saboda haka a takaice akidar siyasar Malam Aminu Kano ta sha bamban nesa ba kusa ba da `yan siyasarmu na yau.

Bambanci ko kuma in ka kwatanta da `yan siyasar yanzu a kasin haka ne, wato su ‘yan siyasar yanzu ba su san ma mene ne `yanci ba, abin da suka sani shi ne tara kudi dan amfanin kansu da `ya`yansu, da matansu, da wadanda suke so su azurta, saboda haka idan ka kwatanta siyasar su Malam Aminu Kano da `yan siyasar yau abin ya sha bamban nesa ba kusa ba saboda canjin zamani da canjin yanayin.

Farfesa, wacce rawa jaridun Hausa za su taka wajen samun nasarar wadannan sabbin tsare-tsare?

To bisa la’akari da yadda muka lura da cewa kafofin yada labarai na Hausa da jaridun Hausa suna da dinbim makaranta da masu bibiyarsu babu shakka, haka za mu hada kai da Jaridun Hausa sosai domin isar da sako a lungu na birni da karkara, ba ma kamar mutanenmu da suke kudancin kasar nan da ma sauran wasu wurare suna bibiyar jaridun Hausa da sauransu. Yanzu ana bibiyarmu ma ta hanyar kafofin sadarwa na zamani, to wannan abu ne da za mu yi iya kokarinmu mu ga mun hada kai da duk wata kafa da sakonmu zai isa duk inda ake bukata gwargwadon hali.

Ana yin hakan ne domin al’umma  su rika samu  suna karantawa a kokarin da muke na wayar da kan al’umma ta kowanne fanni, har ma da abubuwan da suka shafi turanci shi ma sai an yi  da shi, duk da yake mu dai burinmu shi ne masu jin Hausa a ba su damarsu ta karantawa da Hausa da kuma saurare da sauransu, burinmu dai shi ne mu ilmantar da al’umma masu jin Turanci da masu jin Hausa zalla, a wannan cibiya ta nazarin kimiyyar siyasa ta Gidan Mumbayya.

Haka nan muna da dangantaka ko alaka kyakkyawa da kafofin yada labarai na Talbijin, da Rediyo dake nan Kano da muke gabatar da shirye-shirye, a kullum so ake a fadi wani abu domin yada ilimi cikin duniya ta wadanan kafofi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasu Rahotanninmu Na Musamman A 2023: Asalin Garkin Abuja Da Ya Shafe Sama Da Shekara 177 Da Kafuwa

Next Post

Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

Related

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

5 days ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

6 days ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

6 days ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

4 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

4 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

1 month ago
Next Post
Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina - Sarkin Kagarko

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

August 21, 2025
Boniface

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

August 20, 2025
Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

August 20, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

August 20, 2025
Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

August 20, 2025
Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

August 20, 2025
Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

Rajistar Katin Zaɓe: Gwamnatin Kano Za Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Wayar Da Kan Jama’a 

August 20, 2025
Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo

Xizang A Shekaru 60 Da Kafuwa: Daga Mawuyacin Hali Zuwa Farin Wata Sha Kallo

August 20, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Watsi Ga Ƙarin Girma Ga ASP 179, Ta Ɗaga Darajar 952 Zuwa DSP

August 20, 2025
Xi: Wajibi Ne A Aiwatar Da Dabarun JKS Wajen Mulkin Yankin Xizang Na Sin A Sabon Zamani

Xi: Wajibi Ne A Aiwatar Da Dabarun JKS Wajen Mulkin Yankin Xizang Na Sin A Sabon Zamani

August 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.