• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makomar Masarautun Kano Ta Fara Tayar Da Kura A Jihar

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
in Labarai
0
Makomar Masarautun Kano Ta Fara Tayar Da Kura A Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka dai daya daga cikin batutuwan da suka fara tayar da sabuwar kura a farfaijiyar siyasar Jihar Kano shi ne batun makomar masarautun da tsohuwar gwmanatin Abdullahi Umar Ganduje ta kirkira guda hudu da suka hada da Bichi, Rano Gaya da Karaye, bayan warware rawanin tsohon Sarkin Kano na 14, Alhaji Sanusi Lamido Sanusi.

‘Yan Kwankwasiyya na ta shelanta cewa tun da Allah ya ba su wannan dama za su dawo da korarren sarkin, wanda kuma dawowarsa za ta iya zama silar sauke wadancan sarakuna hudun ko makamancin hakan.

  • Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya
  • Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa

 An sha jin jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso mai juya akalar jam’iyyar NNPP a Kano na cewa,  abubuwan da suka alkawarta wa Kanawa a lokacin yakin neman zabe dole su cika su, kuma jam’iyyar ta fara cika alkawari ta hanyar rushe wasu wuraren da suka bayyana cewa an yi ba bisa ka’ida. Haka suma ma’aikatan da Gwamnatin Ganduje ta dauka guguwar wannan sauyi ta yi awon gaba da su.

Ana cikin wannan hali ne kuma kwatsam sai jagoran Kwankwasiyyar ya gabatar da wata hira a kafafen yada labarun Jihar Kano, wanda a cikin tattaunawar aka tambayeshi batun matsayin sarakunan hudu da ake ta ce-ce-ku-ce a kansu, nan take ya bayyana cewa, “Ni ba a yi kowone irin zama kan haka da ni ba, amma dai na san dole za mu zauna mu duba abin da ya kamata a gyara, sai a gyara wanda kuma za a bari sai a bari.

  Ra’ayoyin Mutane… 

Labarai Masu Nasaba

Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Daya daga cikin masu adawa da Gwamnatin Kwankwasiyya, Danbilki Kwamanda ya gabatar da nasa jawabin wanda kuma ya soki gwamnati kan maganar masarautu.

Sai dai wannan kalamai ya sa an kama Kwamanda Danbilki bisa zargin za su iya tunzura al’umma wadanda suka shafi batun masarautun Kano.

Hukumar DSS ce ta fara gayyatarsa tare da mika shi ga jami’an rundunar ‘yan sanda, kamar yadda lauyan da ke kare shi, Barriser Ibrahim Abdullahi ya tabbatar wa da manema labarai a Kano.

Shi ma mai bai wa gwamna shawara kan harkokin addinai II, Gwani Musa Hamza Falaki ya yi karin haske kan ce-ce-ku-ce-cen da ke ta kara ruruwa kan batun masarautun Kano. Ya ce a bangaren Gwamnatin Abba har yanzu lokaci bai yi ba, kuma ba inda ya taba bayyana shirin cire wadancan sarakuna, domin akwai matakai da kowacce gwamnati ke bi wajen warware duk wata matsala da kalubale.

Ya ce Kanawa kowa ya sha kuruminsa domin Gwamnatin Abba babbu abin da ke gabanta illa ci gaban Kanawa, saboda haka duk abin da zai taimaki wa al’umma shi ne babban burin wannan gwamnatin.

A bangaren Amb. Mansur Haruna, wanda yana daga cikin ‘yan jam’iyyar adawa ta APC wadanda suke kallon yunkurin wannan gwamnati bai wuce batun tsige sarakunan da al’umma ke matukar farin ciki da zuwansu ba.

A cewarsa, jama’a sun ga irin ci gaban da aka samu sanadiyyar nada wadannan sarakuna. Ya ce yanzu an ji maganar da jagoaran Kwankwasiyyar ya yi wanda kuma duk abin da ya fada dole shi suke zaton zai faru, saboda haka su a ganinsu sun gama shirye-shiryen tsige wadannan sarakuna da ke zaman alkairi ga Kanawa.

Wadannan su ne abubuwan da a halin yanzu a Jihar Kano ke fuskanta, musamman ganin yanzu gwamantin ta zauna, kuma su akidar Kwankwasiyya ita ce, fada da cikawa. An dai ji kalaman su, inda suke jadadda cewa dukkan alkawuran da suka yi lokacin yakin neman zabe suna kyautata zaton cikawa, har ma sun fara nuna irin wannan matsaya kan wasu kasuwannin Jihar Kano da ma’aikatan da gwamnatin baya ta dauka aiki da kuma batun masarautu, wanda yanzu su ne lamarin da ya fi tayar da hankali a farfajiyar siysar Kano.

Abin da masana ke kokarin nunawa bai wuce ita gwmanatin Abba ta yi kokarin rike matsayinta, sannan kuma ta fuskanci kalubalen da ke gabanta domin guje wa barin jaki a koma dukan taiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tarihin Kano Daga Zamanin Sarki Bagauda (I)

Next Post

Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

Related

Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja
Manyan Labarai

Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja

21 minutes ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

3 hours ago
An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa
Labarai

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

3 hours ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

4 hours ago
Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa
Labarai

Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa

5 hours ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

8 hours ago
Next Post
Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

LABARAI MASU NASABA

Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja

Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja

July 23, 2025
Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin

July 23, 2025
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

July 23, 2025
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

July 23, 2025
An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

July 23, 2025
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

July 23, 2025
Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi

Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi

July 23, 2025
Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa

Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa

July 23, 2025
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

July 23, 2025
Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

July 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.