ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makomar Masarautun Kano Ta Fara Tayar Da Kura A Jihar

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Kano

Yanzu haka dai daya daga cikin batutuwan da suka fara tayar da sabuwar kura a farfaijiyar siyasar Jihar Kano shi ne batun makomar masarautun da tsohuwar gwmanatin Abdullahi Umar Ganduje ta kirkira guda hudu da suka hada da Bichi, Rano Gaya da Karaye, bayan warware rawanin tsohon Sarkin Kano na 14, Alhaji Sanusi Lamido Sanusi.

‘Yan Kwankwasiyya na ta shelanta cewa tun da Allah ya ba su wannan dama za su dawo da korarren sarkin, wanda kuma dawowarsa za ta iya zama silar sauke wadancan sarakuna hudun ko makamancin hakan.

  • Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya
  • Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa

 An sha jin jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso mai juya akalar jam’iyyar NNPP a Kano na cewa,  abubuwan da suka alkawarta wa Kanawa a lokacin yakin neman zabe dole su cika su, kuma jam’iyyar ta fara cika alkawari ta hanyar rushe wasu wuraren da suka bayyana cewa an yi ba bisa ka’ida. Haka suma ma’aikatan da Gwamnatin Ganduje ta dauka guguwar wannan sauyi ta yi awon gaba da su.

ADVERTISEMENT

Ana cikin wannan hali ne kuma kwatsam sai jagoran Kwankwasiyyar ya gabatar da wata hira a kafafen yada labarun Jihar Kano, wanda a cikin tattaunawar aka tambayeshi batun matsayin sarakunan hudu da ake ta ce-ce-ku-ce a kansu, nan take ya bayyana cewa, “Ni ba a yi kowone irin zama kan haka da ni ba, amma dai na san dole za mu zauna mu duba abin da ya kamata a gyara, sai a gyara wanda kuma za a bari sai a bari.

  Ra’ayoyin Mutane… 

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Daya daga cikin masu adawa da Gwamnatin Kwankwasiyya, Danbilki Kwamanda ya gabatar da nasa jawabin wanda kuma ya soki gwamnati kan maganar masarautu.

Sai dai wannan kalamai ya sa an kama Kwamanda Danbilki bisa zargin za su iya tunzura al’umma wadanda suka shafi batun masarautun Kano.

Hukumar DSS ce ta fara gayyatarsa tare da mika shi ga jami’an rundunar ‘yan sanda, kamar yadda lauyan da ke kare shi, Barriser Ibrahim Abdullahi ya tabbatar wa da manema labarai a Kano.

Shi ma mai bai wa gwamna shawara kan harkokin addinai II, Gwani Musa Hamza Falaki ya yi karin haske kan ce-ce-ku-ce-cen da ke ta kara ruruwa kan batun masarautun Kano. Ya ce a bangaren Gwamnatin Abba har yanzu lokaci bai yi ba, kuma ba inda ya taba bayyana shirin cire wadancan sarakuna, domin akwai matakai da kowacce gwamnati ke bi wajen warware duk wata matsala da kalubale.

Ya ce Kanawa kowa ya sha kuruminsa domin Gwamnatin Abba babbu abin da ke gabanta illa ci gaban Kanawa, saboda haka duk abin da zai taimaki wa al’umma shi ne babban burin wannan gwamnatin.

A bangaren Amb. Mansur Haruna, wanda yana daga cikin ‘yan jam’iyyar adawa ta APC wadanda suke kallon yunkurin wannan gwamnati bai wuce batun tsige sarakunan da al’umma ke matukar farin ciki da zuwansu ba.

A cewarsa, jama’a sun ga irin ci gaban da aka samu sanadiyyar nada wadannan sarakuna. Ya ce yanzu an ji maganar da jagoaran Kwankwasiyyar ya yi wanda kuma duk abin da ya fada dole shi suke zaton zai faru, saboda haka su a ganinsu sun gama shirye-shiryen tsige wadannan sarakuna da ke zaman alkairi ga Kanawa.

Wadannan su ne abubuwan da a halin yanzu a Jihar Kano ke fuskanta, musamman ganin yanzu gwamantin ta zauna, kuma su akidar Kwankwasiyya ita ce, fada da cikawa. An dai ji kalaman su, inda suke jadadda cewa dukkan alkawuran da suka yi lokacin yakin neman zabe suna kyautata zaton cikawa, har ma sun fara nuna irin wannan matsaya kan wasu kasuwannin Jihar Kano da ma’aikatan da gwamnatin baya ta dauka aiki da kuma batun masarautu, wanda yanzu su ne lamarin da ya fi tayar da hankali a farfajiyar siysar Kano.

Abin da masana ke kokarin nunawa bai wuce ita gwmanatin Abba ta yi kokarin rike matsayinta, sannan kuma ta fuskanci kalubalen da ke gabanta domin guje wa barin jaki a koma dukan taiki.

Kano
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Next Post
Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.