• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makomar Masarautun Kano Ta Fara Tayar Da Kura A Jihar

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
in Labarai
0
Makomar Masarautun Kano Ta Fara Tayar Da Kura A Jihar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka dai daya daga cikin batutuwan da suka fara tayar da sabuwar kura a farfaijiyar siyasar Jihar Kano shi ne batun makomar masarautun da tsohuwar gwmanatin Abdullahi Umar Ganduje ta kirkira guda hudu da suka hada da Bichi, Rano Gaya da Karaye, bayan warware rawanin tsohon Sarkin Kano na 14, Alhaji Sanusi Lamido Sanusi.

‘Yan Kwankwasiyya na ta shelanta cewa tun da Allah ya ba su wannan dama za su dawo da korarren sarkin, wanda kuma dawowarsa za ta iya zama silar sauke wadancan sarakuna hudun ko makamancin hakan.

  • Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya
  • Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa

 An sha jin jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso mai juya akalar jam’iyyar NNPP a Kano na cewa,  abubuwan da suka alkawarta wa Kanawa a lokacin yakin neman zabe dole su cika su, kuma jam’iyyar ta fara cika alkawari ta hanyar rushe wasu wuraren da suka bayyana cewa an yi ba bisa ka’ida. Haka suma ma’aikatan da Gwamnatin Ganduje ta dauka guguwar wannan sauyi ta yi awon gaba da su.

Ana cikin wannan hali ne kuma kwatsam sai jagoran Kwankwasiyyar ya gabatar da wata hira a kafafen yada labarun Jihar Kano, wanda a cikin tattaunawar aka tambayeshi batun matsayin sarakunan hudu da ake ta ce-ce-ku-ce a kansu, nan take ya bayyana cewa, “Ni ba a yi kowone irin zama kan haka da ni ba, amma dai na san dole za mu zauna mu duba abin da ya kamata a gyara, sai a gyara wanda kuma za a bari sai a bari.

  Ra’ayoyin Mutane… 

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Daya daga cikin masu adawa da Gwamnatin Kwankwasiyya, Danbilki Kwamanda ya gabatar da nasa jawabin wanda kuma ya soki gwamnati kan maganar masarautu.

Sai dai wannan kalamai ya sa an kama Kwamanda Danbilki bisa zargin za su iya tunzura al’umma wadanda suka shafi batun masarautun Kano.

Hukumar DSS ce ta fara gayyatarsa tare da mika shi ga jami’an rundunar ‘yan sanda, kamar yadda lauyan da ke kare shi, Barriser Ibrahim Abdullahi ya tabbatar wa da manema labarai a Kano.

Shi ma mai bai wa gwamna shawara kan harkokin addinai II, Gwani Musa Hamza Falaki ya yi karin haske kan ce-ce-ku-ce-cen da ke ta kara ruruwa kan batun masarautun Kano. Ya ce a bangaren Gwamnatin Abba har yanzu lokaci bai yi ba, kuma ba inda ya taba bayyana shirin cire wadancan sarakuna, domin akwai matakai da kowacce gwamnati ke bi wajen warware duk wata matsala da kalubale.

Ya ce Kanawa kowa ya sha kuruminsa domin Gwamnatin Abba babbu abin da ke gabanta illa ci gaban Kanawa, saboda haka duk abin da zai taimaki wa al’umma shi ne babban burin wannan gwamnatin.

A bangaren Amb. Mansur Haruna, wanda yana daga cikin ‘yan jam’iyyar adawa ta APC wadanda suke kallon yunkurin wannan gwamnati bai wuce batun tsige sarakunan da al’umma ke matukar farin ciki da zuwansu ba.

A cewarsa, jama’a sun ga irin ci gaban da aka samu sanadiyyar nada wadannan sarakuna. Ya ce yanzu an ji maganar da jagoaran Kwankwasiyyar ya yi wanda kuma duk abin da ya fada dole shi suke zaton zai faru, saboda haka su a ganinsu sun gama shirye-shiryen tsige wadannan sarakuna da ke zaman alkairi ga Kanawa.

Wadannan su ne abubuwan da a halin yanzu a Jihar Kano ke fuskanta, musamman ganin yanzu gwamantin ta zauna, kuma su akidar Kwankwasiyya ita ce, fada da cikawa. An dai ji kalaman su, inda suke jadadda cewa dukkan alkawuran da suka yi lokacin yakin neman zabe suna kyautata zaton cikawa, har ma sun fara nuna irin wannan matsaya kan wasu kasuwannin Jihar Kano da ma’aikatan da gwamnatin baya ta dauka aiki da kuma batun masarautu, wanda yanzu su ne lamarin da ya fi tayar da hankali a farfajiyar siysar Kano.

Abin da masana ke kokarin nunawa bai wuce ita gwmanatin Abba ta yi kokarin rike matsayinta, sannan kuma ta fuskanci kalubalen da ke gabanta domin guje wa barin jaki a koma dukan taiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tarihin Kano Daga Zamanin Sarki Bagauda (I)

Next Post

Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

2 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

3 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

4 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

6 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar ÆŠantata

10 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

12 hours ago
Next Post
Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.