ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Makomar Masarautun Kano Ta Fara Tayar Da Kura A Jihar

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Kano

Yanzu haka dai daya daga cikin batutuwan da suka fara tayar da sabuwar kura a farfaijiyar siyasar Jihar Kano shi ne batun makomar masarautun da tsohuwar gwmanatin Abdullahi Umar Ganduje ta kirkira guda hudu da suka hada da Bichi, Rano Gaya da Karaye, bayan warware rawanin tsohon Sarkin Kano na 14, Alhaji Sanusi Lamido Sanusi.

‘Yan Kwankwasiyya na ta shelanta cewa tun da Allah ya ba su wannan dama za su dawo da korarren sarkin, wanda kuma dawowarsa za ta iya zama silar sauke wadancan sarakuna hudun ko makamancin hakan.

  • Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya
  • Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa

 An sha jin jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso mai juya akalar jam’iyyar NNPP a Kano na cewa,  abubuwan da suka alkawarta wa Kanawa a lokacin yakin neman zabe dole su cika su, kuma jam’iyyar ta fara cika alkawari ta hanyar rushe wasu wuraren da suka bayyana cewa an yi ba bisa ka’ida. Haka suma ma’aikatan da Gwamnatin Ganduje ta dauka guguwar wannan sauyi ta yi awon gaba da su.

ADVERTISEMENT

Ana cikin wannan hali ne kuma kwatsam sai jagoran Kwankwasiyyar ya gabatar da wata hira a kafafen yada labarun Jihar Kano, wanda a cikin tattaunawar aka tambayeshi batun matsayin sarakunan hudu da ake ta ce-ce-ku-ce a kansu, nan take ya bayyana cewa, “Ni ba a yi kowone irin zama kan haka da ni ba, amma dai na san dole za mu zauna mu duba abin da ya kamata a gyara, sai a gyara wanda kuma za a bari sai a bari.

  Ra’ayoyin Mutane… 

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Daya daga cikin masu adawa da Gwamnatin Kwankwasiyya, Danbilki Kwamanda ya gabatar da nasa jawabin wanda kuma ya soki gwamnati kan maganar masarautu.

Sai dai wannan kalamai ya sa an kama Kwamanda Danbilki bisa zargin za su iya tunzura al’umma wadanda suka shafi batun masarautun Kano.

Hukumar DSS ce ta fara gayyatarsa tare da mika shi ga jami’an rundunar ‘yan sanda, kamar yadda lauyan da ke kare shi, Barriser Ibrahim Abdullahi ya tabbatar wa da manema labarai a Kano.

Shi ma mai bai wa gwamna shawara kan harkokin addinai II, Gwani Musa Hamza Falaki ya yi karin haske kan ce-ce-ku-ce-cen da ke ta kara ruruwa kan batun masarautun Kano. Ya ce a bangaren Gwamnatin Abba har yanzu lokaci bai yi ba, kuma ba inda ya taba bayyana shirin cire wadancan sarakuna, domin akwai matakai da kowacce gwamnati ke bi wajen warware duk wata matsala da kalubale.

Ya ce Kanawa kowa ya sha kuruminsa domin Gwamnatin Abba babbu abin da ke gabanta illa ci gaban Kanawa, saboda haka duk abin da zai taimaki wa al’umma shi ne babban burin wannan gwamnatin.

A bangaren Amb. Mansur Haruna, wanda yana daga cikin ‘yan jam’iyyar adawa ta APC wadanda suke kallon yunkurin wannan gwamnati bai wuce batun tsige sarakunan da al’umma ke matukar farin ciki da zuwansu ba.

A cewarsa, jama’a sun ga irin ci gaban da aka samu sanadiyyar nada wadannan sarakuna. Ya ce yanzu an ji maganar da jagoaran Kwankwasiyyar ya yi wanda kuma duk abin da ya fada dole shi suke zaton zai faru, saboda haka su a ganinsu sun gama shirye-shiryen tsige wadannan sarakuna da ke zaman alkairi ga Kanawa.

Wadannan su ne abubuwan da a halin yanzu a Jihar Kano ke fuskanta, musamman ganin yanzu gwamantin ta zauna, kuma su akidar Kwankwasiyya ita ce, fada da cikawa. An dai ji kalaman su, inda suke jadadda cewa dukkan alkawuran da suka yi lokacin yakin neman zabe suna kyautata zaton cikawa, har ma sun fara nuna irin wannan matsaya kan wasu kasuwannin Jihar Kano da ma’aikatan da gwamnatin baya ta dauka aiki da kuma batun masarautu, wanda yanzu su ne lamarin da ya fi tayar da hankali a farfajiyar siysar Kano.

Abin da masana ke kokarin nunawa bai wuce ita gwmanatin Abba ta yi kokarin rike matsayinta, sannan kuma ta fuskanci kalubalen da ke gabanta domin guje wa barin jaki a koma dukan taiki.

Kano
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.