ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, September 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afirka

Mummunar manufar nan kan bakin haure da shugaba Donald Trump na kasar Amurka ya bullo da ita ta jefa dubban baki dake zama a kasarsa cikin mawuyacin hali na kaskanci, yayin da matakin ya raba dubban baki da iyalansu, sabo da yadda ake bi sako da lungu ana farautar bakin mazauna Amerika ba tare da bin ka’ida ba.

Da dama wadanda aka kame a matsayin bakin hauren ba su cikin rukunin wadanda suka cancanci kora. Wato irin wadanda ke zama Amerika ba tare da cikakkun takardu ba, ko wadanda bizarsu ta kare, ko kuma wadanda suka aikata miyagun laifuka, kamar su fashi da makami, hada-hada da miyagun kwayoyi, sata ko zamba cikin aminci da makamantansu.

To yanzu dai shugaba Trump ya rasa yadda zai yi da wadannan dubban bakin haure da aka kame, amma a ganinsa akwai mafita, wato ta tursasawa kasashen Afirka da su karbi bakuncin wadannan bakin haure, idan kuma suka ki amincewa, to shugaba Trump ya sha alwashin kakaba harajin cinikayya a kan wadannan kasashe.

ADVERTISEMENT

Yanzu haka dai Sudan ta kudu ta ba da kai, domin kuwa tuni har wani rukunin bakin hauren su takwas sun sauka birnin Juba, babban birnin Sudan ta kudu. Daya ne tak dan asalin Sudan ta kudu, sauran kuwa sun hada da ’yan kasashen Myammar, Cuba da Vietnam. Akasarinsu dai mutanen da suka aikata muggan laifuka ne, kuma suka shafe shekaru da dama a gidajen kurkuku na Amerika.

Kazalika, shugaba Trump ya yi yunkurin turo irin wadannan bakin haure ’yan asalin Venezuela zuwa Nijeriya, amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba. Nan take dai ma’aikatar kula da harkokin wajen Nijeriya ta ki amincewa da wannan bukata. Nijeriya ba za ta zama jujin da Amerika za ta jibge sharar bakin haurenta ba, wadanda akasarinsu tsaffin masu aikata muggan laifuka ne wadanda suka kwashe shekara da shekaru gidan kaso. Don haka abar Nijeriya ta ji da matsalar da ke gabanta na yaki da rashin tsaro, ba wai a kara ingizo mata karin matsala ba.

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Babban abin dubawa a nan shi ne ko mene ne hikimar tura irin wadannan bakin haure zuwa kasashen Afirka? Misali kamar bakin hauren da Amerika take son turawa Nijeria, ’yan asalin kasar Venezuela, ko kuma bakin hauren da Sudan ta kudu ta karba ’yan asalin Myammar, da Cuba da Vietnam, al’adunsu da harshensu sun sha banban da na ’yan Afirka. Sabo da haka babu wata alaka tsakanin juna.

To idan ba domin isgilanci da gadara ba, ta yaya Mr. Trump zai nemi tursasawa kasashen Afirka karbar irin wadannan bakin haure maimakon ya tasa keyarsu zuwa kasashensu na asali?(Lawal Mamuda)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Na Hanyar Siliki Karo Na 13 A Xi’an
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kammala Taro Na 13 Na Dandalin Tattauna Tsaro Na Xiangshan A Beijing
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su
  • Sulaiman
    An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui
  • Sulaiman
    Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf
  • Sulaiman
    NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

MASU ALAKA

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka
Ra'ayi Riga

Ra’ayin Kasar Sin Kan Fasahar AI Yana Samar Da Damammaki Ga Afirka

September 14, 2026
Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Next Post
An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

An Yi Wa Ƴan Mata  Fiye Da 754,000 Rigakafin Cutar Sankarar Mahaifa

LABARAI MASU NASABA

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

Manyan Abubuwa 7 Da Za A Na Tuna Wa Da Tsohon Gwamnan Kogi Marigayi Ibro

September 20, 2026
Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su

Sin Ta Harba Tauraron Dan’adam Na Gwaji Da Ya Hade Ayyukan Sadarwa Da Tattara Bayanai Da Sarrafa Su

September 20, 2026
Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha

Kano Pillars Ta Lallasa Doma United Da Ci 4-1 A Sani Abacha

September 20, 2026
Osimhen Ba Zai Buga Wa Nijeriya Wasannin Madagascar Da Guinea-Bissau Ba

Osimhen Ba Zai Buga Wa Nijeriya Wasannin Madagascar Da Guinea-Bissau Ba

September 20, 2026
An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui

An Bude Taron Masana’antun Kere-Kere Na Duniya Na Shekarar 2026 A Hefei Na Lardin Anhui

September 20, 2026
Tinubu Ya Janye Shirin Halartar UNGA, Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya

Tinubu Ya Janye Shirin Halartar UNGA, Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya

September 20, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Sabbin Hare-Hare A Filato

September 20, 2026
Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf

Kwankwaso Ya Ce A Shirye Yake Ya Sasanta Gwamna Yusuf

September 20, 2026
NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

NSCDC Ta Kama Mutane Biyar Kan Zargin Sayar Da Naman Mushen Shanu A Yobe

September 20, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Radda Ya Ƙaddamar Da Shirin Tsaron Abinci Da Tallafawa Matasa A Katsina

September 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.