• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Allah Ya Yi Rantsuwa Da Girman Darajar Manzon Allah S.A.W (2)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
1 year ago
in Dausayin Musulunci
0
Allah Ya Yi Rantsuwa Da Girman Darajar Manzon Allah S.A.W (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An karbo daga Abdullahi bin Abbas (RA) cewa ma’anar Yaasiyn tana nufin “Ya kai Dan Adam cikakke, tana nufin Annabi Muhammadu (SAW)”. Manzon Allah (SAW) Dan Adam ne cikakke. Har ila yau Abdullahi bin Abbas (RA) din ya fada a ruwayarsa cewa Yaasiyn tana nufin rantsuwa ce da sunan Annabi. Kuma tana daga cikin sunayen Allah. Allah ya dauki sunan ya baiwa Manzon Allah (SAW). Mun taba yin bayani kan sunayen Allah da Allah Ta’ala ya baiwa Manzon Allah (SAW) a wani darasinmu da ya gabata, irin su Ra’ufu da Rahimu.

Malam Dajjaju (Malamin Larabci, mutumin Bagadad) ya ce kila an ce ma’anar Yaasiyn tana nufin sunan Manzon Allah ne kai tsaye, wato ‘Muhammadu’ (SAW). To idan haka ne, kalmar ta Yaasiyn daga yaren Siriyananci ne; yaren Annabi Ibrahim (AS) kamar irin su ‘Ahiyyan Sharahiyyan’ da ke nufin ‘Hayyun Kayyum’, Manzon Allah (SAW) ya fade su. To ita ma kalmar Yaasiyn tana daga cikinsu, ma’anarta da larabci ita ce ‘Muhammadu’ (SAW), idan an koma Siriyananci kuma sai a ce ‘Yaasiyn’.

  • Allah Ya Yi Rantsuwa Da Girman Darajar Manzon Allah S.A.W (1)
  • Allah Ya Amintar Da Zuciyar Manzon Allah (SAW) Tare Da Tausasawa

Kila kuma aka ce ma’anarta (Yaasiyn), tana nufin ‘Ya kai cikakken mutum’. Kila kuma aka ce tana nufin ‘Ya kai Dan Adam cikakke’, wanda ya fadi wannan ya yi daidai da fassarar Abdullahi bin Abbas (RA). An karbo daga Sayyidina Muhammadu Dan Hanafiyyatu (Dan Sayyidina Aliyu Karramallahu wajhahu ne. Bayan rasuwar Sayyada Fadimah (AS), Sayyidina Aliyu ya yi aure da yawa. Lokacin da aka yi Yakin Musulaimatul Kazzab Sayyidina Aliyu ya samu kuyanga ‘yar kabilar Hanafiyyah, ita ce ta haifi shi Muhammadul Hanafiyya. Bai fi shekara biyu da wafatin Annabi SAW ba aka haife shi sai Sayyidina Aliyu ya sanya masa sunan Manzon Allah SAW. Akwai bayanai da yawa a kansa kamar sauran ‘yan’uwansa) cewa ma’anar Yaasiyn tana nufin ‘Ya Muhammadu’ (SAW). Ka ga a nan, Sayyidina Muhammadul Hanafiyya da Malam Dajjaju fassararsu ta zo daya cewa Kalmar Yaasiyn tana nufin ‘Ya Muhammadu’.

An karbo daga Malam Ka’abul Ahbari cewa ma’anar Yaasiyn rantsuwa ce da Allah ya yi (da Kalmar) tun kafin ya halicci sama da kasa da shekara dubu biyu. Kila haka ya gani a cikin Attaura. Malam Alkadiy Iyad ya ce to idan an kadarta cewa ‘Yaasiyn’ na daga cikin sunayen Manzon Allah (SAW) kuma karatu ya inganta cewa rantsuwa ce, to za a gane akwai girmamawa cikin wannan maganar dangane da abin da ya rigaya da Allah Ta’ala ya ce ya rantse da rayuwar Manzon Allah (SAW). Wato ma’anar haka, Allah ya rantse da rayuwar Manzon Allah kuma ya rantse da sunansa (SAW) kana ya tabbatar da cewa Annabi Muhammadu (SAW) Manzonsa ne (SWT) kamar yadda ya zo a farko-farkon Suratu Yaasiyn. Dama akwai wurare da dama da Allah (SWT) yake jera rantsuwa a cikin Alkur’ani. Kamar yadda muka gani a nan ya rantse da Alkur’ani kana kuma ya rantse da rayuwar Manzon Allah (SAW). Wannan magana tana karfafuwa sosai saboda Allah ya dora rantsuwa kan rantsuwa ta hanyar amfani da harafin ‘wawun na adafi’ (harafin sada kalma). Daga nan sai aka fahimci cewa lallai ayar farkon (Yaasiyn) ita ma rantsuwa ce.

Idan kuma an ce Allah ya kira sunan Manzon Allah ne, ma’ana ya ‘Yaasiyn’ da ke nufin ya Muhammadu ko sauran fassarar sunan da muka kawo bayanansu a baya; to Allah ya zo da wata rantsuwa kuma bayan haka domin tabbatar da Annabcinsa (SAW). Allah ya kira sunansa an ji shi kuru-kuru sai kuma ya rantse don tabbatar da Manzancin Manzon Allah (SAW) da shaidawar cewa Manzon Allah shiryayye ne (a ayar da Allah ya ce kai kana daga cikin Ma’aika kuma a kan tafarci madaidaici). Ubangiji maigirma da daukaka ya rantse da sunan Manzon Allah da Littafinsa (Alkur’ani) cewa shi Manzon Allah yana daga cikin Ma’aika bisa wahayin da ya yi masa zuwa ga bayinsa. Kuma bayan Manzon Allah yana daga ciki Ma’aika har ila yau yana kan hanya madaidaiciya daga imaninsa, ma’ana yana kan hanyar da babu karkata a cikinta a kan gaskiya.

Labarai Masu Nasaba

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Malam Nakkashu ya ce Allah bai rantse a kan kowa daga cikin Annabawa kan manzancin da ya aiko su da shi ba a cikin Littafinsa (Alkur’ani) sai Manzon Allah (SAW). Kowane Manzo da aka aiko idan mutanensa sun karyata shi; shi Manzon da kansa ne yake basu amsa. Amma da kafiran Annabi Muhammad (SAW) suka karyata shi Allah ne da kansa ya rantse kusan sau shida ya ce lallai shi (Annabi Muhammadu) Manzonsa ne. Allah ba ya sa wasa a cikin komai nasa, koda bai rantse ba kawai amsa ya bayar cewa Annabi Muhammadu Manzonsa ne ya isa amma kuma saboda karfafa abin sai ya yi ta zubo rantsuwa. A wata fahimtar kuma aka ce dalilin da ya sa Allah ya yi rantsuwar a kan tabbatar da Manzancin Annabi (SAW) shi ne: a Shari’ar da ya saukar ma wannan al’umma ya umurci mai kare kansa a gaban shari’a ya yi rantsuwa. To tunda kafiran Makka sun karyata Manzancin Manzon Allah (SAW), a maimakon shi ya yi rantsuwa don kare Manzancin nasa sai Allah da kansa ya yi hakan saboda girman darajar Manzon Allah a wurinsa (SWT). Wannan duka ya tafi a bisa salsalar fassarar da aka yi wa ‘Yaasiyn’ a matsayin ‘Shugaba’. Kuma Wannan din ya tabbata a cikin Hadisi ingatacce wanda Manzon Allah (SAW) ya ce “Ni ne shugaban Dan Adam duka kuma ba alfahari nake ba (ina gode wa Ubangijina ne).

Wata ayar kuma da ke nuna rantsuwar da Allah ya yi da Manzon Allah (SAW) ita ce farkon Suratul Balad.

Harafin ‘Laa’ da ta zo a farkon ayar wasu malamai musamman Malam Makkiy sun fassarata da cewa Allah (SWT) yana nufin “Ba domin kai (Ya Rasulallah) kana cikin wannan garin ba; ba zan rantse da shi ba”. Ko kuma “Ina rantsuwa da wannan garin ne saboda kana ciki amma idan ka fita daga cikinsa ba zan rantse da shi ba”. A wata aya ta cikin Suratun Nisa’i Allah ya nuna a lokacin da Manzon Allah (SAW) ya fita daga garin (Makka) ya koma Madina kamar shi ma (SWT) ya koma can. Domin ayar ta ce “…duk wanda ya fita daga gidansa yana mai yin Hijira zuwa wurin Allah da Manzons”. A Akidarmu Allah yana ko ina amma kuma babu kamar inda Masoyinsa Manzon Allah (SAW) yake. Wannan ai ya isa girman Manzon Allah, Allah ya ce ba zai rantse da Makkah ba idan ba ya ciki (kamar yadda wannan fassarar take nuni).

Kila kuma an ce wannan harafin na ‘Laa’ kara magana ne. Muma a Hausa muna da irin wannan. Kamar misali wani zai ba da amsa kan wani abu da aka tambaye shi ko ya aikata wani abu? Sai ya ce “a’a, ban yi ba ko a’a wallahi ba zan yi ba”. Duk wannan (a’a) kari ne. To kila wannan ‘Laa’ din karin magana ne. Don haka ma’anar ayar tana nufin Allah yana cewa “ina rantsewa da wannan garin. Idan kana ciki”. Wato Allah zai rantse da Makkah Idan Manzon Allah (SAW) yana ciki. Ko kuwa Allah ya ce “zan rantse da wannan garin saboda kai (SAW)”. Ko kuma ba zaman Manzon Allah a Makka Allah yake nufi ba (a ayar), Allah yana nufin ya halatta wa Manzon Allah garin na Makkah domin ita haramun ce ga kowa. Ko da gini mutum zai yi sai ya kasance akwai wata bishiya da yake so ya sare, ba zai sare ba sai an yi masa kudin fansa ya biya. Haka idan aka kashe dabba. Kamar misali mutum ya kashe bauna to dole sai ya biya da saniya. Sai dai za a iya karya baure kamar yadda Abbas (RA) ya tambayi Manzon Allah (SAW) a kai ya amince a yanke. Koda laifi mutum ya yi ya shiga yankin da Allah ya haramta ba za a shiga ciki a kama shi ba sai dai a yi masa talala, kamar a hana shi abinci har yunwa ta koro shi ya fito daga ciki saboda girman Makkah. To amma Manzon Allah (SAW) aka halatta wa ita. Shi ma ya ce na awa daya ne tak a lokacin da za a yi Fatahu Makkata. Wannan duka saboda fito da ma’anar yadda wasu suka fassara ayar ta biyu ce mai kalmar ‘hillu’ da cewa ana nufin hallata garin ne ga Annabi (SAW) ba zamansa a ciki ba, kamar yadda malaman da suka tafi a kan wannan Tafsirin suka bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jirgin Shugaban Kasa Na Ci Gaba Da Lakume Makudan Kudade Wajen Kula Da Shi

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

2 weeks ago
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)
Dausayin Musulunci

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

3 weeks ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)
Dausayin Musulunci

Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)

4 weeks ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

1 month ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

2 months ago
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci
Dausayin Musulunci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

2 months ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

July 11, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar

July 11, 2025
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

July 11, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.