ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani and Sulaiman
8 months ago
Annabi

… ci gaba daga makon da ya gabata.

 

Tanan za a fahimci cewa, duk masu ikirarin guluwwi da tahdidi karya suke, duk wannan aya ta “caffa da Annabi” da Ubangiji ya ce, da shi aka yi, ta karyata su.

ADVERTISEMENT

4 – Allah ya hada girmansa da girman Annabinsa (Walillahil izzatu wali rasulihi…), ya kara hada yardarsa da yardar Annabinsa (Wallahu warasuluhu a hakku an yurduhu), Allah da Annabinsa shi yafe cancanta a yarda da shi. Ubangiji in yana magana da Annabinsa, lamiri daya yake amfani da shi ba na mutum biyu ba. Wani Hadisi ya zo, yana bayar da labarin wani abu da ya faru tsakanin wanin masanin zance da Annabi SAW, kila an ce ya Annabin Allah, ga wani masanin zance yana so zai yi maka zance, sai aka amince masa hakan, daga cikin zancensa, ya bayyana cewa, “duk wanda ya yi wa Allah da Annabinsa biyayya, ya tsira; wanda duk ya bijerewa Allah da Annabinsa, ya hallaka, (Man Adahuma fakad rashada, wa man Asahuma fakad gawa)”, sai Annabi SAW ya kore shi. Da yawan

Malamai masu sharhin wannan Hadisi, suna cewa, wannan hukuncin Annabi ne da ya zartar amma su ba su ga kuskuren da ya yi ba. Bangaren Sufaye suka amsa cewa, sun gano inda ya yi kuskure, Ubangiji in zai hada kansa da Annabinsa, Lamirin abu daya yake amfani da shi amma wannan masanin zance, da Lamirin abu biyu ya yi amfani da shi a gaban Annabi SAW da fadinsa (Adahuma da Asahuma a maimakon Adahu da Asahu). Amma Annabi SAW da ya iya karatun, cewa ya yi, “Allah wa rasuluhu harrama bai’al Kamri – Allah da ma’aikinsa ya hana kasuwancin giya”, don haka, duk wanda ya ce, zai rabe tsakanin Allah da Annabinsa, to ya kuka da kansa.

LABARAI MASU NASABA

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

Al’ummar Annabi SAW, Malama ce wayayya, ba za ta taba daukar Annabi SAW ya zama kishiyar Allah ba. Mutum ne mai girma da Allah ya girmama shi. Don kana tarayya da wani babban mutum aka da yaushe, ba zai sa ka zama shi ba. Annabi SAW wani mai girma ne da Ubangiji ya girmama shi har karatu ya kasa fahimtar kusancin shi da Ubangiji (Dana fatadalla, fakana kaba kausaini au adna).

5 – Allah ya saka amsa masa, amsa wa Annabinsa ne SAW (Ya Ayyuhallazina amanu istajibu lillahi walirrasuli iza da’akum – ya ku wadanda kuka yi imani, ku amsa kiran Ubangiji da na Annabinsa idan sun kira ku…

6 – Allah Ubangiji ya hori Annabi SAW ya yi fito-na-fito da kowace sura ta Alkur’ani, mafi karamar sura ta Alkur’ani, itace me aya Uku (Suratul Kausar), don haka, kowace sura a Alkur’ani ta zama “Mu’ujiza”,  da wannan lissafi za mu fahimci cewa, duk aya Uku ta Alkur’ani Mu’ujiza ce!

Muhyiddeen Arabi, ya ce, duk Aya Daya fannin wani ilimi ce, Shehu Ibrahim Inyass ya ce gaskiya ne amma akwai aya Daya na samu fannin ilimi tara acikinta, itace (Falizalika fad’u, wastakim kama umirta, wala tattabi’i ahwa’ahum, wakul amantu bima anzalallahu minal kitab, wa umirtu li a’adila bainakum, Allahu rabbuna wa rabbukum, lana a’amaluna walakum a’amalukum, la hujjata bainana wa bainakum, Allahu yajma’u bainana, wa ilaihil masir – yi kira akan wannan alkairan da aka baka, tsaya kamar yadda aka umurceka, kar ka bi son zuciyarsu, ka ce ka yi ka yi imani da abinda Ubangijinka ya saukar maka daga Alkur’ani, an umarce ni in yi adalci a tsakanin ku, Allah shi ne Ubangijinmu kuma shi ne Ubangijinku, babu wanda za a yi masa hisabi da aikin wani na sharri amma alkairin wasu na shafar wasu, babu wata hujja tsakaninmu da ku, Allah zai hada mu daku a ranar Alkiyama, duk wurin Ubangiji dai za mu tafi.

Mu tafi a cewa, duk aya Uku, mu’ujiza ce, akwai ayoyi fiye da 6,000 a Alkur’ani, in muka raba 6,000+ gida uku, za mu samu mu’ujiza 2,000+ acikin Alkur’ani.

Annabi Musa AS, Ubangiji ya ambace shi da cewa, ya ba shi mu’ujiza 9 amma Annabi SAW, a Alkur’ani mun samu 2,000+. Don haka, ba sai an yi tawili ba, a fili yake, Annabi SAW ya fi duk sauran Annabawan Allah. Sannan kuma, duk mu’ujizozin sauran Annabawa, zamani na tsawo suna kara shudewa, amma na Annabi SAW zamani na tsawo suna kara bayyana.

Cewa, mu’ujizozin Annabi SAW sun fi na sauran Annabawa, hakan ya nuna cewa, ya fi duk sauran Annabawa.

Annabi
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ posts Bio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Falalar Neman Tsari Daga Sharrin Shaidan
Annabi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Dausayin Musulunci

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 3, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)
Dausayin Musulunci

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Falalar Haɗa Basmala da Suratul Fatiha

June 19, 2026
Next Post
Sanya Dokar Ta -Ɓaci Kan Tsaro Bai Da Amfani – Datti Baba-Ahmed

Sanya Dokar Ta -Ɓaci Kan Tsaro Bai Da Amfani - Datti Baba-Ahmed

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.