ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
6 months ago
Annabi

Assalamu alaikum ‘yan uwa masoyan Annabi Muhammad SAW, fiyayyen halitta, yau shafinmu zai yi tsokaci ne kan yadda Annabi SAW ya zarce duk sauran Annabawa yawan mu’uzijoji.

14 – Fifiko tsakanin Annabawa ya danganta ne da wasu abubuwa kamar haka:

– Yawan Mu’ujizozi: wanda ya fi yawan mu’ujiza ya fi girman daraja. Mu’ujiza tana nuna gaskiyar Annabi a bisa isar da sakonsa. Mu’ujizar Annabi SAW a Alkur’ani kadai, ta haura 2,000+, ina kuma sauran da ya nuna wa Sahabbansa?

ADVERTISEMENT
  • An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa
  • Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Wani sahabi mai suna, Abu zur’atar radi ya ce, Annabi SAW ya rasu yana da sahabbai kimanin 124,000, kuma kowanne sahabi acikin wannan adadin ya ga akalla mu’ujiza daya ta Annabi SAW, da haka za mu iya cewa, mu’ujizozinsa SAW sun haura 124,000 don haka ya kere dukkan Annabawa mu’uzija.

Yana daga cikin sananniyar mu’ujizarsa SAW, abinci dan kadan, ya sanya masa albarka, jama’a da yawa su yi taci har su bar shi, sai in ya taba shi, sai mutum daya ma ya karasa cinye abincin.

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

Wata rana, Abu Huraira (RA) yunwa ta kama shi matuka, har yazu wurin mimbarin Annabi SAW da ke cikin masallacin Annabi, sai ya fadi a wurin, duk wadanda suka zo wurin suka ganshi, sai suce Allah Sarki, wane ba shi da lafiya har sai da Annabi ya zo ya ganshi, sai yace masa, Abu Hurairah kana jin yunwa ko? Sai ya amsa da eh. Take Annabi SAW ya ce masa, biyo ni zuwa daki na. Annabi yasa aka kawo masa nono a dan koko kamar yadda aka saba, Abu Hurairah yana jira a ce masa ya sha, sai Annabi SAW ya ce masa ya kira ‘yan uwansa Ahlul suffati, kuma jama’a ne masu yawa, da isowarsu, Annabi SAW ya sa wa Nonon albarka, suka fara sha, tawaga bayan tawaga, har sai da kowa ya sha ma’ishi, babu wanda ya yi saura sai Annabi SAW da Abu Huraira, sai ya ce, Abu Huraira fara sha iya shanka, sannan ya ci gaba da ce masa, kara sha, kara sha, har sai da Abu Huraira ya ce, na rantse da wanda ya aiko ka, ya ishe ni, sannan Annabi SAW ya karba ya yi Bismillah ya sha sannan ya kare.

Don haka, wata rana, Annabi SAW ya ta shi ya yi kuka yana tuna masoyansa a gaban Sahabbansa, sai suka ce, ya Rasulullah ba mu ne masoyanka ba, sai ya ce, A’a ku Abokaina ne, wadan can sun yi imani da ni, ba suga mu’uzija ko daya ba, ku kuma kun yi imani da ganin irin wannan abu: Nono dan kadan, a shayar da tawaga da shi, ruwa ya fito ta tsakanin ‘yan yatsu, halittarsa mai kyau, sadaukanta, jarumta, Ilimi, fasaha, cika alkawari, Amana, kyauta, ga su nan da yawa ba iyaka.

A yakin Kandak, lokacin da Sayyadina Aliyu ya kashe Amru bin Waddu (mai karfin kasar Larabawa gaba daya a zamanin) bayan ya yi wa Sayyadina Ali rawani, ya ba shi takobin shi sannan ya ce “rabbi la tazarni farda wa anta kairul warisin”, bayan ya kashe shi sai Annabi ya tambaye shi, ya kake jin kanka a yanzu? Sai ya ce, ina jin da za a tattara min mutanen Madina, zan iya kashe su gaba daya! Sai Annabi SAW ya ce masa, to shirya, akwai wani Saurayi sadauki zai fito daga wannan dajin, za ku yi yaki. Bayan fitowar saurayi sadauki, sai ya tambaya, kai ne Ali? wurinka aka turo ni, yau daya ne zai tsira tsakanin ni da kai, bayan gwabzawa, saurayi ya yi wata wujijjiga da Sayyadina Ali, nan take ya ga ne cewa, wannan saurayi ba kowa ba ne face SAW. Don babu wani da ya isa ya yi wa Sayyadina Ali irin haka duk duniya sai Annabi SAW, sai ya fahimci cewa, akwai sama da shi. Fakrurrazi mai Hadisi ne ya fitar da wannan Hadisin.

15 – Annabi Adam da duk ‘ya’yansa Annabawa suna karkashin tutar Annabi Muhammad SAW a ranar Alkiyama: wannan ya tabbatar cewa, duka Annabawa suna kasa da shi. Ya zo cikin Hadisi Annabi SAW yana cewa, “ana sayyadi waladi Adam wala fakr – ni ne shugaban ‘ya’yan Annabi Adam ba alfahari ba”, sabida Manzon Allah SAW, zuciyarsa tana da fuska biyu – yadda yake kallon hadarar Allah da yadda ya ke kallon bayin Allah. Don haka, Annabi SAW in yana gaban Ubangiji, sunan shi “Abdu”, amma in ya taho wurinmu sauran bayi, shugabanmu ne. Annabi Yahya a wurinmu ma, Ubangiji kiranshi ya yi da cewa, “Sayyidan wa hasuran wa nabiyyan minassalihin – Shugaba, katangagge kuma Annabi daga cikin managarta bayi”

A wani wuri kuma, Annabi SAW ya ce, babu wanda zai shiga Aljannah daga Annabawa kafinsa SAW, kuma babu wata al’umma da za ta shiga daga al’ummomin da suka gabata kafin al’ummarsa SAW! Duka wannan saboda albarkar Annabi SAW.

An ruwaito hadisi daga Anas bin Malik yana cewa, manzon Allah SAW ya ce, “ni ne farkon halitta wanda zai fara fita daga kabari idan an tashi al’umma a ranar Alkiyama, ni ne wanda zan wakilce su wurin yin bayani a gaban Ubangiji don kowa ya tsira, ni ne zan yi musu bushara idan gwiwoyinsu sun sage sun ga kamar ba za su tsira ba, tutar godiya tana hannuna, ni ne mafi girman dan Adam a wurin Ubangijina, kuma ba alfahari nake ba, cewa aka yi in fada, “wa amma bini’imati rabbika fahaddis – ka bayyana ni’imomin Ubangijinka a gareka”.

Wannan magana da Annabi ya fada wa Sahabbansa, ita muke kira da Maulidi. A tara Jama’a a fada musu girma da darajar fiyayyen halitta, Annabi Muhammad SAW.

An karbo Hadisi daga Abdullahi bin Abbas yana cewa, wasu daga cikin sahabban Annabi SAW sun taru suna hirar karatu, sai wasu suka ce, ” ittakazallahu Ibrahima kalila – mamakin yadda Allah ya riki Annabi Ibrahim Badadi (Kalila)”, wasu kuma suka ce, “wannan ai ba abin mamaki ba ne, kamar yadda Ubangiji ya yi hira da Annabi Musa, – wakallamallahu Musa taklima,” wasu kuma suka ce, ina kuka bar Annabi Isa, “Kalimatullahi wa ruhuhu – Kalmar Allah kuma ruhinsa yadda ya dace da shi”, wasu kuma Adamu “isdafahu – Allah ya zabe shi”, kuma duk babu wanda ya san Annabi SAW yana jinsu.

Da Annabi SAW, ya fahimci abun na su ya ki kare wa kuma suna shirin fadawa hadari, sai ya fito ya dakatar da su, ya ce musu, na ji duk batutuwanku da hujjojinku, kuma duk abinda kuka fada haka ne! Kun ce, “Annabi Ibrahim Kalilullah, Musa kalimullahi wa najiyyahu, Adamu isdafahu, duka haka ya ke, amma duk ku saurara kuji! Ni Habibullahi ne ba alfahari ba, saboda mukamin na shi ne! Ni nake rike da tutar godiya, ni ne wanda zai yi ceto, ni ne farkon wanda za a karbi cetonsa a ranar Alkiyama, ba alfahari ba! Ni zan fara kwankwasa kofar Aljannah don a bude, sai a bude in shiga, tare da ni akwai Mu’uminai fukara’u.

Don haka, ya tabbata a hadisi, ranar Alkiyama, ana neman ceto, kowa ya dimauce, sai a tafi wurin Annabi Adam, ya ce, ba ni ba, sai a tafi wurin Annabi Musa, shi ma ya ce ba ni ba, a tafi wurin Annabi Isa, shi ma haka, a tafi wurin Annabi Ibrahim shi ma haka, amma dai a tafi wurin Rasulullah SAW.

A ranar Alkiyama, bayan Annabi SAW ya bude kofar shiga Aljannah, Shahidai za su taho zuwa shiga Aljannah, sai a tambayesu, waye ya kira ku? Sai suce Malamai suka gaya mana cewa, mune farko, sai a ce musu, to kubari Malamai su fara shiga; Malamai da jin haka, sai su ta so za su shiga, sai a tambayesu, ku su waye? Sai su ce, mu ne Malamai, to ya aka yi kowa bai zama Malami ba sai ku kadai, sai suce, saboda duk sun tafi wurin neman abinci muka muna wurin koyon ilimi, to ku ba ku cin abinci? Muna ci, wasu ne suka dauki nauyin cin abincinmu, to ku bari masu ciyarwa su fara shiga. Don haka, sai mai ciyarwa ya fara shiga Aljannah, sannan Malami sannan Shahidi.

Annabi SAW, ya kara ce musu, kuma ni ne mafificin mutanen farko da na karshe, ba alfahari ba!

Annabi
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ postsBio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)

MASU ALAKA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Dausayin Musulunci

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

May 29, 2026
Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
Dausayin Musulunci

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

May 22, 2026
Annabi
Dausayin Musulunci

Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci

May 15, 2026
Next Post
Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji

Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.