• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Kashe Saurayinta Saboda Ya Hana Ta Kason Damfarar Da Suka Yi

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
Ta Kashe Saurayinta Saboda Ya Hana Ta Kason Damfarar Da Suka Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an rundunar ‘yansanda a Jihar Imo sun kama wata mata ‘yar shekara 27 mai suna Oluchi Nzemechi bisa zarginta da daba wa saurayinta, Kelechi Nzemechi, wuka har lahira sakamakon wata rigima da ta kaure tsakaninsu a kan kin ba ta kasonta na kudin da suka yi damfara ta intanet.

Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ‘Yansandan Jihar, Henry Okoye, wanda ya bayyana hakan ga manema labarai a Owerri a lokacin da yake gabatar da wacce ake zargin, ya ce Oluchi ta amsa laifin kashe saurayin nata ne kan kin ba ta kaso daga sama da kudin kasar Indonesiya miliyan 250 da suka damfari wani mutum dan kasar.

  • Dan Takarar Gwamnan Katsina A NNPP Ya Ba Da Tallafin Miliyan 50 Ga ‘Yan Gudun Hijira
  • CDD Ta Soki NBC Kan Cin Tarar Trust TV Da Wasu Miliyan 20

Da take bayar da labarin mummunan al’amarin, rundunar ‘yansandan ta bayyana cewa wacce ake zargin ta yi ikirarin cewa saurayin nata da ta kashe ya gabatar da ita ga wanda za su damfara har ta kai ga sun samu wadannan kudade, inda ta kara da cewa ta yi amfani da wuka a kicin wajen daba masa wuka bayan da suka yi zazzafar gardama.

“Rundunar ‘yansandan ta gudanar da bincike mai zurfi sun cafke wata budurwa ‘yar shekara 27 mai suna Oluchi Nzemechi da ke unguwar Uzoagba a Karamar Hukumar Ikeduru ta Jihar Imo da laifin daba wa abokin aikinta, Kelechi Nzemechi, mai shekaru 31 wuka wanda ya kai shi ga mutuwa.

“Yayin da take amsa tambaya, wacce ake zargin ta amsa laifinta, ta yarda cewa masoyinta ne ya yaudare ta inda ya jefa hanyar damfarar intanet mai suna ‘yahoo yahoo’.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

A ranar 02/06/2024, ta yi zazzafar husuma da shi saboda ya kasa ba ta wani kaso na kudin da ake zargin ta kai Rupiah Miliyan 250 da suka samu daga hannun wani da suka damfara a Indonesia, inda daga nan ne ta yi amfani da wukar kicin ta daba masa wuka a wani bangare na jikinsa,” in ji ‘yan sanda.

A lokacin da take zantawa da ‘yan jarida, Oluchi ta bayyana yadda ta yi kokarin wanke kanta daga kashe shi ta hanyar rubuta wasikar yaudara, “A kokarin da na ke na boye laifina, na yi gaggawar rubutawa a takarda; ‘Kana tunanin za ka ci kudina ka tafi haka, ni uwa ce ga samari, ina zuwa don neman matarka da yaronka har da danginka. Sai na dora takardar a kan gawar sannan na gudu daga gidan,” in ji ta.

Wacce ake zargin ta kuma bayyana cewa tana zaune da wanda ta kashe tun shekarar 2019 inda suka haifi yaro tare. ASP Okoye ya ce za a gurfanar da wacce ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Amurka Ta Sake Yada Karairayi Ta Hanyar Zargin Sin Da Tallafawa Rasha Da Makamai

Next Post

Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

7 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

8 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

9 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

10 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

13 hours ago
Next Post
Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.