• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Shekarar 2024: Barr. Nyesom Ezenwo Wike

by Leadership Hausa
6 months ago
in Labarai
0
Gwarzon Shekarar 2024: Barr. Nyesom Ezenwo Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Barrister Nyesom Ezenwo Wike, wanda aka fi sani da “Mr. Project”, ya samu lambar yabo ta Jaridar LEADERSHIP saboda irin gudummawarsa wajen samar da ci gaba ta hanyar samar da ababen more rayuwa ga al’umma a yankunan karkara da birane.

A matsayinsa na ministan babban birnin tarayya, ya kawo sauye-sauye masu yawa, wanda hakan ya sa ya zama jagora mai hangen nesa da jajircewa.

  • Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf
  • Gwarzon Gwamnan 2024: Sanata Bala Mohammed

Tarihi da Karatunsa

An haifi Wike a garin Rumuepirikom, Obio-Akpor da ke Jihar Ribas, a ranar 13 ga Disamba, 1967. Ya karatu a sakandaren gwamnati a Eneka, daga nan ya shiga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Ribas (RSUST), inda ya samu digiri na farko a fannin Shari’a (Law). Bayan haka, ya halarci makarantar koyon aikin lauya (Law School) a shekarar 1997, kuma daga bisani ya samu digiri na biyu a Siyasa da tsare-tsare (Political and Administrative Studies) daga wannan jami’a.

Shigarsa Siyasa

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

Wike ya shiga harkokin siyasa a 1999, lokacin da ya zama shugaban ƙaramar hukumar Obio-Akpor, wanda ya yi shekaru takwas yana mulki. Daga bisani ya zama Shugaban ma’aikata na gwamna Rotimi Amaechi. A shekarar 2011, an naɗa shi ƙaramin Ministan Ilimi a ƙarƙashin gwamnatin Goodluck Jonathan, inda ya kai matsayin Ministan Ilimi mai cikakken iko a 2013.

A matsayinsa na minista, ya kawo sauye-sauye masu mahimmanci a tsarin ilimi a Nijeriya. Ya kuma jagoranci sauyin manufofin da suka inganta damar samun ingantaccen ilimi a duk faɗin Nijeriya.

Gwamnan Jihar Ribas

A ranar 29 ga Mayu, 2015, Wike ya zama Gwamnan Jihar Ribas, inda ya gudanar da ayyukan ci gaba masu tarin yawa. A cikin shekaru takwas na mulkinsa, ya gabatar da ayyukan gine-gine da samar da hanyoyi da inganta lafiya da kuma haɓaka ilimi. Ya kuma tabbatar da biyan albashin ma’aikata akan lokaci da biyan kuɗaɗen ‘yan fansho da tsofaffin ma’aikata. Ya ƙaddamar da ayyukan da suka shafi rayuwar mutanen jiharsa masu muhimmanci, ciki har da samar da hanyoyin mota da gadaje da titunan a birane da karkara. Wannan ya sauya fuskar Jihar Ribas, hakan ya sa al’umma suka amince da jagorancinsa.

Matsayin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT)

An naɗa Wike a matsayin ministan babban birnin tarayya (FCT) a ranar 16 ga Agusta, 2023. Da hawansa wannan matsayi, ya yi duba na musamman kan ayyukan da aka fara amma ba a kammala ba a Abuja. Ya gano manyan matsaloli, musamman waɗanda suka shafi rashin isassun kuɗaɗe, sannan ya ɗauki matakan gaggawa don magance su.

A matsayinsa na minista, Wike ya tabbatar da shugabanci mai kyau wajen bayar da kwangiloli, yana mai cewa ba zai bayar da kwangila ba, ba tare da an tabbatar da kuɗin da ake da su ba a ƙasa ba. Wannan ya kawo gaskiya da inganci a tsarin gudanarwa. Ya gina hanyoyi,

da asibitoci da makarantu a sassa daban-daban na Abuja, ya kuma tabbatar da cewa kowanne yanki ya amfana da shugabancinsa.

Haka kuma, ya sake farfaɗo da filin jirgin saman Abuja na biyu, wanda ya kawo sauƙi ga zirga-zirgar jiragen sama. Ya kuma samar da ingantaccen tsarin sufuri wanda ya rage cunkoso da bunƙasa kasuwanci a Abuja.

Walwalar Ma’aikata da Aikace-aikace

A ƙarƙashin jagorancinsa, Wike ya tabbatar da biyan albashin malaman makaranta da sauran ma’aikata da ya gada a matsayin bashi. Har ila yau, ya inganta walwalar ma’aikata ta hanyar ƙarawa sama da 1,000 girma, wanda hakan ya ƙara musu kwarin gwuiwa. Wike ya tabbatar da cewa ya bai wa sha’anin tsaro fifiko, inda ya haɗa kai da hukumomin tsaro da ƙungiyoyin sa kai don tabbatar da zaman lafiya a Abuja. Wannan ya rage yawan laifuka a birnin, kuma ya ƙara ƙwarin gwuiwar jama’a kan aikin hukumomin tsaro.

Salon Jagorancinsa

Kowa ya san Minista Wike, gwani ne wajen bai wa jama’a kula. Yana ziyartar wuraren gudanar da ayyuka, yana sauraron ƙorafe-ƙorafen jama’a, sannan yana tabbatar da cewa an magance matsalolin da suka taso cikin ƙanƙanin lokaci. Wannan salon jagoranci ya sa jama’a suka gamsu da da irin shugabancinsa.

A yau, Minista Wike ya kafa tarihi a babban birnin tarayya ta fuskar aiyukansa na bunƙasa hanyoyin more rayuwa da walwalar jama’a da tsaro, wanda hakan ya tabbatar da cewa yana da hangen nesa da jajircewa wajen bunƙasa Abuja. Wannan lambar yabo tana nuna yadda ya ke amfani da jagorancinsa wajen kawo ci gaba mai ma’ana ga jama’arsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Shekarar 2024: Mallam Umar A. Namadi

Next Post

Hukumar Gwamnati Mafi Ƙwazo A Shekarar 2024: Hukumar Ilimin Bai-ɗaya (UBEC)

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

1 hour ago
bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

3 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

6 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

7 hours ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Labarai

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

7 hours ago
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
Labarai

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

8 hours ago
Next Post
UBEC

Hukumar Gwamnati Mafi Ƙwazo A Shekarar 2024: Hukumar Ilimin Bai-ɗaya (UBEC)

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.