• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)

by Muhammad
8 months ago
in Labarai
0
Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Adams Oshiomhole fitaccen ɗan siyasa ne a Nijeriya, kuma Tsohon Gwamnan Jihar Edo. Yanzu haka, shi ne Sanatan da ke wakiltar Edo ta Arewa. Jagoranci da ƙwarewarsa a fannin siyasa sun taka rawar gani sosai a siyasar Nijeriya, musamman a zaɓen Gwamnan Jihar Edo na 2024, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasarar ɗan takarar Jam’iyyar APC, Sanata Monday Okpebholo.

An haifi Oshiomhole a ranar 4 ga watan Afrilun 1952, a Jihar Edo. Ya fara aikinsa a matsayin mai fafutukar kare haƙƙin ma’aikata, inda ya zama Shugaban Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC). A lokacin da yake shugabancin NLC, ya tsaya tsayin daka wajen kare haƙƙin ma’aikata, ya kuma jagoranci tattaunawa kan muhimman manufofi, wanda ya sa aka san shi a matsayin jagora mai tsayin daka.

  • Ɗangote Ne Gwarzon Jaridar LEADERSHIP Na Shekara Ta 2024
  • Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf

A shekarar 2008, ya zama Gwamnan Jihar Edo, bayan hukuncin kotu. A lokacin mulkinsa, ya mayar da hankali kan inganta ababen more rayuwa da kiwon lafiya da ilimi, ciki har da shahararren shirinsa na “Red Roof Revolution,” wanda ya gyara makarantu a faɗin jihar. Salon mulkinsa na kula da jama’a ya sa ake girmama shi sosai.

A shekarar 2018, an naɗa shi shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, inda ya tallafa wa jam’iyyar kuma ya goyi bayan gwamnatin Shugaba Buhari. Duk da ƙalubalen cikin gida, jagorancin Oshiomhole ya taimaka wajen samun nasarori a zaɓuɓɓuka masu muhimmanci.

A matsayinsa na Sanata, ya mayar da hankali kan ci gaban ababen more rayuwa, bai wa matasa dama, da samar da ayyukan yi mazaɓarsa. Har yanzu yana da tasiri a wajen al’amur ƙasa da na yankinsa, inda yake amfani da ƙwarewarsa a fannin mulki da fafutuka.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

Sadaukarwar Oshiomhole wajen yi wa jama’a hidima da rawar da ya taka a fagen siyasar Nijeriya ya sa ya cancanci zama Gwarzon Ɗan Siyasa na Shekarar 2024 na Jaridar Leadership.

Tsarin shugabancinsa na samar da ci gaba da bai wa al’umma ƙwarin gwiwa yana matuƙar tasiri a ƙasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: #GwarzonShekara2024 #Award2024 #Leadership #LeadershipAward #LabaraiAdams Oshiomhole
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwarzon Gwamnan Shekara Ta 2024: Alhaji Abba Kabir Yusuf

Next Post

Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

Related

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

58 minutes ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

4 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

14 hours ago
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

15 hours ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

17 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

18 hours ago
Next Post
Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.